Kano: Manoma sun koka kan rabon taki
Manoman jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya sun koka dangane da aniyar gwamnatin na rabon taki ta hanyar kai wa mazabu.
A baya dai ana raba takin ne ta hanyar tsarin wayar tafi-da-gidanka.
Korafin da manoman suke yi dai shi ne idan aka ce za a kai takin zamanin zuwa mazabu to 'yan jam'iyya mai mulki ne kawai za su samu.
Sai dai kuma gwamnatin ta musanta hakan a inda ta ce za a kai takin zamanin mazabu ne a domin mutane su yi saurin samu kafin damina ta kankama.