Boko Haram: Shugaban Chadi ya ba Shekau zabi
Shugaban kasar Chadi, Idriss Deby ya bukaci shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau, ya mika wuya ga soji ko kuma a kashe shi.
Mr Deby ya yi ikirarin cewa ya san wurin da Shekau ke boye.
Deby ya bayyana haka ne a lokacin da shugaban Nijar, Mahamadou Issoufou, ya kai masa ziyara a birnin Ndjamena.
Ya ce, "Idan Abubakar Shekau na son kansa da lafiya, to ya mika wuya; mun san inda yake. Idan bai mika wuya ba, makomarsa za ta zama iri daya da sauran mabiyansa."
Rikicin Boko Haram wanda aka soma a Najeriya a yanzu ya shiga makwabtan kasashe kamarsu Chadi da Kamaru da kuma Nijar.
Mutane fiye da 13,000 ne suka rasu tun da aka soma rikicin Boko Haram a Najeriya.