Pillars da Nasarawa United sun raba maki
Kungiyar Kano Pillars ta tashi wasa kunnen doki 1-1 tsakanin ta da Nasarawa United a wasan mako na 16 a gasar Firimiyar Nigeria da suka yi a ranar Laraba.
Pillars ce ta fara cin kwallo ta hannun Mubarak Said a minti na tara da fara tamaula, yayin da Nasarawa United ta farke ta hannun Adamu Hassan bayan da aka dawo daga hutu.
Sai a ranar Alhamis Lobi Stars za ta karbi bakuncin Akwa United.
Ga sakamakon wasanni tara da aka buga a ranar Laraba:
- Rangers 1-1 Remo
- Wikki 1-0 Enyimba
- Rivers 0-0 Plateau
- ABS 1-1 Gombe
- MFM 2-1 Abia Warriors
- 3SC 1-0 El-Kanemi
- FCIU 1-0 Tornadoes
- Sunshine 2-0 Katsina