An dakatar da tattaunawar mika mulki a Sudan
Jagoran gwamnatin soji da ke mulkin Sudan ya ce an dakatar da tattauwar da ake yi da Jagororin da ke son tabbatar da mulkin dimokradiyya a kasar ta tsawon sa'oi 72.
Da ya ke jawabi ta gidan talbijin din kasar, Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya ce za a kawar da shingayen da masu zanga-zanga suka sanya akan tituna a khartoum nan bada jimawa ba.
Wannan na zuwa ne sa'o'i kadan bayan bangarorin biyu sun amince da kafa gwamnatin hadaka da mika mulki ga farar hula.
A jiya laraba an yi ta jin karar harbe-harbe da aka yi amanna sojoji ne ke yi dan firgita masu zanga-zanga su cire shingayen da suka kafa a hedikwatarsu da ke birnin Khartoum.
Masu zanga-zangar dai sun ce akalla mutane 9 aka ji wa rauni, sai dai kawo yanzu babu wani sahihin adadi.
Tashin hankali irin wannan da ya barke a ranar litinin ya yi sanadin mutuwar masu bore 6, inda suka kafe dole a hukunta sojojin da suka yi harbin.