Got a TV Licence?

You need one to watch live TV on any channel or device, and BBC programmes on iPlayer. It’s the law.

Find out more
I don’t have a TV Licence.

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza da Ahmad Tijjani Bawage

time_stated_uk

  1. Rufewa

    Karshen rahotanni kenan a wannan shafi na kai-tsaye.

    Sai kuma gobe Alhamis idan Allah ya kai mu.

    Ahmad Bawage ke cewa mu kwana lafiya.

  2. Sojojin Isra'ila sun ce mutumin da ake zargin ya daɓawa bayahude wuƙa ya rasu

    Sojojin Isra'ila sun ce mutumin da ake zargi da daɓawa wani bayahude wuƙa a wani hari kan mazauna yankunan yahudawa 'yan kama-wuri-zauna a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan ya mutu bayan harbe shi.

    An bayyana cewa dan Isra'ilan da aka daɓawa wukar yana cikin yanayi mara tsanani.

    Kawo yanzu dai jami'an gwamnatin Isra'ila ba su yi ƙarin haske ba game da wanda ake zargi da kai harin.

    A baya-bayan nan dakarun tsaron Isra'ila sun harbe wani mayaki Bafalasɗine a lokacin wani farmaki da suka kaddamar a wani sansanin 'yan gudun hijira da ke birnin Nablus a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan.

    Wannan dai shi ne Bafalasɗine na biyar da dakarun tsaron Isra'ila suka kashe a gabashin kudus tun a farkon wannan shekara.

  3. Ina ji a jikina zan zama shugaban ƙasa - Tsohon madugun 'yan tawayen Ivory Coast

    Mr Goudé

    Tsohon madugun ‘yan tawayen Ivory Coast da aka wanke daga zarge-zargen cin zarafin bil Adama, ya ce yana ji a jikinsa wata rana zai zama shugaban kasar.

    A taron ‘yan jarida na farko da ya gudanar bayan komawarsa gida daga gudun hijira a watan Nuwamba, Charles Blé Goudé, ya ce zai tsaya takara a zaben shugaban kasar da za a yi cikin shekara ta 2025.

    An mika shi ga kotun hukunta manyan laifukan ƴaki ta duniya shekaru tara da suka gabata, kuma a 2019 ne aka wanke shi tare da tsohon shugaban kasar Laurent Gbagbo.

    Dukkan mutanen biyu ana zarginsu da aikata laifukan keta hakkin dan adam a lokacin tashin hankalin da ya barke bayan zaben kasar na 2010.

  4. 'Matsalar tsaro na ƙara kamari a yankin gabashin Sokoto'

    Mazauna yankin gabashin jihar Sokoto sun ce matsalar tsaro na kara kamari a yankin a baya-bayan nan.

    Sun ce ‘yan fashin daji sun kwashe kwanaki a makon nan suna cin karensu ba babbaka ta hanyar kisa da lalata dukiya da kuma garkuwa da mutane.

    Ku danna kasa domin sauraron rahoton Haruna Shehu – Tangaza.

    Video content

    Video caption: Ku danna hoton sama don sauraron rahoton
  5. Ana ci gaba da taƙaddama kan wanda ke iko da garin Soledar

    Soledar

    Ana ci gaba da samun takaddama game da wanda ke rike da ikon garin Soledar da ke gabashin Ukrane, wanda ke kara fuskantar yaki.

    Shugaban kasar Urkraine, Volodymyr Zelensky, ya ce ana ci gaba da gwabza yaki a garin, inda ya kara da cewa sojojin Rasha sun lalata mafi a-kasarin garin.

    Bugu da kari, shugaban sojojin haya na kamfanin Wagner na ƙasar Rasha, ya sake yin ikirarin kwace iko da garin.

    Yayin da Igor Konashenkov mai magana da yawun ma'aikatar tsaron Rasha ke cewa dakarunsu na ci gaba da luguden wuta inda rundunonin sojin sama suka yi wa Soledar ƙofar rago daga arewa da kuma kudancin garin.

    Dakarun saman na Rasha na ci gaba da kai hare-hare kan inda abokan gaba suka ja daga.

  6. 'Yan sanda a Anambra sun gano gawarwakin mutanen da 'yan bindiga suka kashe

    Police

    Wata haɗakar aiki tsakanin sojoji da 'yan sanda a Anambra, ya samu nasarar gano gawarwakin mutane huɗu a garin Eziani da ke Karamar Hukumar Ihiala na jihar.

    Jaridar daily Trust a Najeriya, ta ruwaito cewa gawarwakin sun kunshi maza uku da mace ɗaya. Ana zargin cewa 'yan bindiga ne suka kashe su a wani hari da suka kai garin inda suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.

    Kakakin 'yan sandan jihar ta Anambra, DSP Ikenga Tochukwu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce tsaurara samamen 'yan sanda da kuma sojoji a Ihiala da makwabtan garuruwa.

  7. MDD ta yi tir da kisan jami'an agaji a Kudancin Sudan

    UN

    Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da kisan jami'an agaji a wasu hare-hare guda biyu da aka kai Kudancin Sudan.

    A cikin wata sanarwa da muƙaddashin kodinetan ba da agaji na MDD a ƙasar, Peter van der Auweraert ya fitar, ta ce ba za su amince da wannan kisa ba, ya kamata kuma a dakatar da shi.

    An harɓe tare da kashe wasu jami'an agaji biyu a bakin aiki lokacin da wasu maƴaka suka far wa ƙauyen Rumameer a Abyei mai albarkatun man fetur da ƙasashen Sudan da kuma Kudancin Suda ke faɗa a kai da ke kan iyaka.

    A wata sanarwa da ofishin ba da agaji na MDD ya fitar ranar Laraba, ta ce an kuma kashe fararen hula da dama a harin.

    Kudancin Sudan dai tana ci gaba da zama wuri mai haɗari ga jami'an ba da agaji, inda a shekarar 2022 kaɗai, an kashe jami'an bayar da agaji tara a bakin aiki, idan aka kwatanta da biyar da aka kashe a 2021.

    Ofishin ba da agaji na MDD, ya ce tun soma rikici a 2013, jami'an ba da agaji 141 ne wanda yawanci 'yan Kudancin Sudan suka rasu yayin bayar da taimako ga mutane.

  8. Yan adawa a Benin sun lashe kujerun majalisar dokoki

    Benin Polls

    Sakamakon wucin gadi na zaben 'yan majalisar dokokin da aka gudanar a ranar Lahadi a ƙasar Benin, ya nuna 'yan adawa sun samu nasarar koma wa majalisar bayan shafe shekaru hudu ba tare da su ba.

    Hukumar zaben ta ce 'yan adawa sun samu kujeru 28 tare da abokan shugaba Patrice Talon da suka samu 81.

    Ana sa ran sakamako na ƙarshe a cikin wannan makon.

    An haramtawa 'yan adawar Benin tsayawa takara a zaben 2019 inda aka ɗaure akasarin masu adawa da Mr Talon a gidan yari wasu kuma suka yi gudun hijira.

  9. Kotu ta ce a biya 'yar sandar da aka kora saboda ta yi ciki diyya

    Court

    Kotun sasanta rikicin ma'aikata a yau Laraba, ta kori hukuncin sashi na 127 na rundunar 'yan sandan Najeriya na 2020 da ya buƙaci korar wata jami'ar 'yar sanda da ta yi ciki ba tare da aure ba.

    'Yar sandar mai suna Omolola, ta kalubalanci korarta a kan zargin cewa hukumomin 'yan sanda sun musguna mata tun da ba a kori takwarorinta maza ba da suka aikata irin laifinta.

    Sai dai a wani hukunci da mai shari'a D.K Damulak na kotun sasanta ma'aikata a Akure ya yanke a ranar Alhamis, ya ce bangaren 'yan sandan da ya bukaci ƙorar 'yar sandar da ta yi ciki, yana cike da musgunawa da kuma ba a yi shi bisa ka'ida ba.

    A cewar kotun, sashin dokar 'yan sandan, ya saɓawa sashi na 42 na kundin tsarin mulki da kuma sashi na 2 na hukumar ƙare hakkin dan adam wanda ya yi watsi da cin zarafi na jinsi.

    Alkalin ya ce dokar ‘yan sanda ba za ta iya tsayawa ba saboda ba ta aiki kan ‘yan sandan da ba su yi aure ba da suka yi wa mata ciki, saboda haka suka yi watsi da ita.

    Alkalin ya umurci a biya 'yar sandar diyyar naira miliyan 5 saboda take hakkinta na ‘yancin yin walwala.

  10. 'Yan sandan Najeriya na neman mutumin da ake zargi da shayar da jaririya tabar wiwi

    Rundunar ‘yan sandan Najeriya na neman wani mutum da ake zargi ya shayar da wata jaririya tabar wiwi, a wani faifan bidiyo da ya bazu a shafin Twitter a ranar Litinin.

    Jami’in hulda da jama’a na rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi ta Twitter, ya ce, dole ne a hukunta wanda ake zargi da aikata babbar ta’asar ga jaririyar.

    Ku danna kasa domin sauraron rahoton wakilinmu na Legas Umar Shehu Elleman.

    Video content

    Video caption: Ku danna hoton da ke sama domin sauraron rahoton
  11. Buhari ya sanya hannu kan kudurin lafiyar kwakwalwa

    Buhari

    Shugaba Muhammadu Buhari, ya sanya hannu kan kudurin lafiyar kwakwalwa da aka gabatar tun 2021 bayan da ta kasa tsallake muhawara tun 2003 zuwa 2013.

    Majalisun tarayyar ƙasar sun yi muhawara a kan kudurin a 2021.

    Shugaban kwamitin harkokin lafiya na majalisar dattawa, Ibrahim Oloriegbe, ne ya tabbatar da amincewa da kudurin da Buhari ya yi a shafinsa na twita.

    View more on twitter

    Kudurin dai zai kare hakkin masu lalurar kwakwala kamar haramta cin zarafinsu a bayar da gidaje da samar da aikin yi da kulawar lafiya da sauran abubuwa.

    Har ila yau, kudurin zai tabbatar da ganin cewa masu lalurar kwakwalwa na da damar irin jinya da za a yi musu sannan babu tirsasawa.

    Wasu abubuwa da suke kunshe cikin dokar sun haɗa da samar da asusun lafiya na masu lalurar kwakwalwa da kirkiro da sashin lafiya a ma'aikatar lafiya ta ƙasa da kuma kirkiro da kwamitin sa ido kan masu lalurar da sauransu.

  12. Hauhawar farashi ta kai adadin da ba ta taɓa kai wa ba cikin shekara 22 a Ghana

    kaya

    Hauhawar farashin kayayyaki a Ghana ta ƙaru da kashi 54.1 cikin ɗari a watan Disamban da ya gabata, adadi mafi yawa da ya taɓa kai wa cikin shekara 22.

    Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito hukumar ƙididdiga ta ƙasar na cewa ƙarancin man fetur da abinci da sauran kayyaki ne suka haddasa tashin farashin.

    Ƙasar Ghana wadda ke yankin yammacin Afirka na fama matsin tattalin arziki a 'yan shekarun nan.

    A bara darajar kuɗin ƙasar ya karye, lamarin da ya ƙara haddasa hauhawar farashin, yayin da gwamnati ta rage yawan kuɗin da take kashewa, kuma ƙarin kuɗin ruwa da babban bankin ƙasar ya yi, ya gaza kawo ƙarshen matsalar.

    Hauhawar farashi da aka samu cikin watan Disamba shi ne mafi muni tun shekarar 2001.

    A watan Yulin bara ne ƙasar ta buƙaci Asusun Bayar da Lamuni na Duniya IMF da ya taimaka mata bayan da tashin farashi da matsin tallalin arziki suka haddasa zanda-zanga a ƙasar.

  13. An yi sabuwar dokar haramta wa likitoci yajin aiki a Zimbabwe

    likitoci

    An haramta wa ma'aikatan lafiya a Zimbabwe shiga yajin aikin da ya zarta sa'o'i 72, inda waɗanda suka saɓa dokar za su iya fuskantar hukuncin ɗaurin wata shida, kamar yadda sabuwar dokar ta nuna.

    Ƙungiyar likitocin ƙasar da kuma ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam sun ce sabuwar dokar za ta ƙara 'dagula' al'amura a ƙasar, tare da tilasta wa likitocin neman aiki a ƙasashen waje.

    Likitoci da ma'aikatan jinya a ƙasar dai sun sha shiga yajin aiki kan matsalar albashi da ƙarancin kayan aiki da magunguna.

    Kusan ma'aikatan lafiya 4,000 ne aka ƙiyasta cewa sun ajiye aiki a ƙasar ake kuma zargin sun nemi aiki a ƙasashen ƙetare a shekarar da ta gabata.

  14. Ɗan Chinan da ake zargi da kashe Ummita ya fara gabatar da shaidu a gaban kotu

    Daga Zaharadden Lawan

    Ummita

    A yau ne ɗan ƙasar Chinan nan da ake zargi da kashe budurwarsa mai suna 'Ummita' a jihar Kano da ke arewacin Najeriya ya fara gabatar da shaida a shari'ar da ake yi masa.

    Hakan ya zo ne bayan masu ƙara sun kammala gabatar da na su shaidun a gaban babbar kotun jihar.

    A zaman babbar kotun na yau, mai shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya ci gaba da sauraren tuhumar da ake yi wa Mista Geng Quangrong da kashe tsohuwar budurwarsa Ummulkhuksum Sani Buhari wadda aka fi sani da 'Ummita'.

    Mista Geng ya tsaya a gaban kotun a matsayin shaida, ya bayyana wa kotun yadda suka haɗu da Ummulkhuksum inda yace wata ƙawarta ce ta ba ta lambarsa ta kira shi cewa tana ƙaunarsa kuma za ta aure shi, shi kuma ya amince.

    Sai dai bayan an ɗauki lokaci suna soyayya tare da kashe mata maƙudan kuɗaɗe sai ta ƙi auren sa, inda ta auri wani amma duk da haka lokaci zuwa lokaci tana kiransa su gaisa ta nemi kuɗi ya ba ta a cewar Mista Geng.

    Barista Abdullahi Maji na daya daga cikin lauyoyin da ke kare Mista Geng ya kuma shaida wa BBC cewa ''ya bayyana wa kotun lokacin da suka fara haɗuwa lokacin yana Delta, ta samu lambarsa daga hannun ƙawarta, ta gayyace shi ya zo Kano, sun ha ɗu faga nan kuma sun fara soyayya tsakaninsu.

    ''Ya yi maganar cewa aƙalla ya kashe mata naira miliyan 60, ta ci kuɗaɗe da yawa daga wajensa, kama daga kuɗaɗen soyen mota da na fili da na fara kasuwancin duka shi ya bata, kuma kamar yadda ya bayyana akwai bayanan kididdigar banki na kuɗin da ya kashe mata, kuma kamar yadda ya faɗa za su tabbatar da haka idan an karɓo su daga banki'', in ji lauyan mista Geng.

    Kazalika, Mista Geng ya ci gaba da faɗaw a kotun cewa ya taɓa ba ta naira miliyan 10 ta sayi mota, amma sai ta yi amfani da kuɗin ta sayi fili a Abuja ta fara gini a 2021.

    Amma daga ƙarshe saboda ba ta son ta aure shi sai ta ce ba ta karɓi komai daga hannun sa ba.

    Har wayau Mista Geng ya shaida wa babbar kotun cewa a ranar 13 Satumba 2022 ta buƙaci ya bata kuɗi ta kammala aikin ginin ta a Abuja.

    Inda shi kuma ya faɗa mata cewa ba shi da kuɗi abin da ya fusatata ta dai ɗaukar wayarsa, sannan ya ƙara da cewa duk maganar da suka yi tana cikin WhatsApp dinsa.

    Mista Geng yace yana matuƙar ƙaunar Ummulkhuksum, ba ya son ɓacin ranta.

    Sannan ya faɗa wa kotun cewa ta rika yin ƙorafin cewa ba ya kashe mata kuɗi kamar baya inda ta tambaye shi ko ba shi da kuɗi ne.

    Daga bisani kuma ta faɗa masa cewa ta samu wani mutum da suke soyayya har ma ta aika masa da hotunan sabon saurayinta, al’amarin da ya ba shi haushi.

    Ɓangaren masu gabatar da ƙara sun ce suna bibiyar bayanan da Mista Geng yake bayarwa a kotu sau da kafa.

    Hajiya Aisha Mahmud darakta ce a ma’aikatar shari’a ta jihar Kano ta yi ƙarin haske bayan fitowa daga kotun.

    ''Tun wancan zaman da muka ce mu mun rufe sai ya nemi kotu da ta ba shi damar ya sake kirowa shaidunsa, tare da neman kotu da ta sake kirawo shaidun da muka gabatar, inda ka kira mahaifiyar yarinyar ta zo ya yi mata tambayoyi, da ɗan sanda shi ma ya zo ya yi masa tambayoyi''

    ''Mu ba mu san yawan sahidun da zai kira ba, yau dai ya fara, to sai goben in ya gama kiran shaidun nasa, zai rufe gobe'', inji Hajiya Aisha

    Alkalin babbar kotun mai shari’a Sanusi Ado Ma’aji ya ɗage zaman kotun zuwa gobe goma sha biyu ga wannan watan don ci gaba da sauraron Mista Geng kan abin da ya faru tsakaninsa da Ummulkhuksum, wadda ake zargin ya kashe ta.

  15. Babban lauyan gwamnatin Peru na gudanar da bincike kan shugaban ƙasar da ministoci

    Babban lauyan gwamnatin Peru, wato attorney-janar ya fara gudanar da bincike a kan shugaban kasar da kuma manyan ministoci, bayan mummunan tashin hankalin da aka kwashe makonni ana yi tsakanin masu zanga-zangar kin jinin gwamnati da kuma jami'an tsaro.

    Tuhumar da zai yi ta hada da ta zargin laifin kisan kiyashi da kuma ta kisan kai.

    An yi ta zanga-zanga tun bayan da aka daure jagoran masu ra'ayin kawo sauyi na kasar ta Peru, Pedro Castillo a watan da ya gabata.

    Firaminista Alberto Otárola, ya ce manufar gwamnatin ita ce dawo da zaman lafiya;

    Tashin hankalin ya fi muni a birnin Juliaca na kudancin kasar, inda aka sanya dokar hana fita a yanzu.

    Masu zanga-zangar na son ganin Shugaba Dina Boluarte ta sauka, amma kuma majalisar dokokin kasar ta goyi bayan sabuwar gwamnatin inda ta kada kuri'ar amincewa da ita.

  16. 'Yan sanda sun kama fasto kan garkuwa da kansa don karɓar kuɗi a wajen mabiyansa

    police

    Rundunar 'yan sandan jihar Plateau da arewa ta tsakiyar Najeriya ta kama wani fasto bisa zargin yin garkuwa da kansa domin karɓar kuɗi a wajen mabiyansa.

    A wata sanarwa da rundunar 'yan sandan jihar ta fitar ta ce Faston mai suna Albarka Bitrus ya haɗa baki da wasu ne ya ɓoye kansa domin ya karɓi kuɗin fansa a wajen mabiyansa.

    Sanarwar ta ce an kama faston tare da waɗanda ya haɗa hannu da su wajen aikata wannan laifi bayan da suka samu bayanan sirri da ke cewa tuni mabiya cocin suka biya naira 600,000 a matsayin kuɗin fansa.

    “Bayan samun labarin garkuwa da faston, da biyan nairan 400,000 da 200,000 daban-daban a matsayin kuɗin fansa domin sakinsa, sai lamarin ya fara bai wa mutane shakku'' kamar yadda sanarwar 'yan sandan ta bayyana

    Sanarwar ta ci gaba da cewa ''Bayan samun bayanan sirri, sai baturen 'yan sanda na Nassarawa Gwong ya gayyaci faston, nan take aka fara gudanar da bincike, inda kuma faston ya tabbatar da cewa ya haɗa baki ne da wasu ne domin ya karɓi kuɗi a wajen mabiyansa''..

  17. Mutum shida sun jikkata a harin tashar jirgin ƙasa a birnin Paris

    'yan sanda

    Hukumomi a birnin a ƙasar Faransa sun ce wani mahari ya soki mutum shida da wani makami a tashar jirgin ƙasa ta birnin Paris da ke ƙasar Faransa, kafin daga bi-sani 'yan sanda su harbi shi tare da kama shi.

    Tashar jirgin ƙasan mai cike da cunkoson mutane ta kasance babbar tashar jiragen ƙasa da ke zirga-zirga zuwa arewacin Faransa da Landan da kuma arewacin Turai.

    Jami'an 'yan sanda na ɗaukar suka da wuƙa a matsayin yunƙurin kisan kai, a maimakon harin ta'addanci, kamar yadda wata majiya ta bayyana.

    Kawo yanzu dai ba a san manufar maharin ba.

    ''Ɗaya daga cikin mutum shidan da maharin ya soka na cikin matsanancin hali, yayin da sauran biyar ɗin suka samu ƙananan raunuka'', kamar yadda mai shigar da ƙara ya bayyana.

    Ministan cikin gida na ƙasar ya shaida wa manema labarai cewa ''duka duka lamarin ya auku ne cikin mintuna biyu''.

    Kawo yanzu ba a san wane irin makami maharin ya yi amfani da shi ba.

    Da fari 'yan sanda sun ce wuƙa ce, sai dai daga bi-sani ministan cikin gidan ya ce ba wuƙa ba ce, wani mummunan makami ne.

  18. Gwamnatin Najeriya za ta samar da jami'an tsaro don kare tasoshin jiragen ƙasa

    jirgin ƙasa

    Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta samar da jami'an tsaro na musamman da za su riƙa kula da sufurin jiragen ƙasa a wani ɓangare na matakan magance hare-haren da ake kai wa jiragen da fasinjoji a ƙasar.

    Ƙaramin ministan sufuri na ƙasar Ademola Adegoroye ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyara tashar jirgin ƙasa ta Tom Ikimi a ƙaramar hukumar Igueben da ke jihar Edo, wadda 'yan bindiga suka kai wa hari a ƙarshen makon da ya gabata tare da yin garkuwa da fasinjoji.

    A wata sanarwa da jami'in hulɗa da jama'a na hukumar sufurin ƙasar ya fitar, ya ce gwamnatin ƙasar za ta ɗauki matakan da suka dace domin magance matsalar hare-hare kan tasoshin jiragen ƙasa domin tabbatar da kariya ga fasinjoji da kayayyakin aikin hukumar.

    Daga cikin matakan da ya ce hukumar za ta ɗauka har da haɗa kai tsakanin hukumar da al'umma mazauna yankunan da tasoshin jiragen suke domin samar da tsaro da tasoshin jiragen.

    Haka kuma ministan ya yi watsi da fargabar da ake yi na cewa gwamnati za ta rufe zirga-zirgar jiragen ƙasa a faɗin ƙasar, yana mai cewa gwamnatin tarayya da hukumar sufurin jiragen ƙasa ba su da wannan niyya, sanna kuma za a ci-gaba da sufurin.

  19. An ɗauki bidiyon 'yan sanda suna yunƙurin yin fashi da makami

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar Kenya sun yaɗa wani bidiyo da kyamarorin tsaro na CCTV suka ɗauka da ke nuna lokacin da wasu jami'an 'yan sandan ƙasar huɗu ke yunƙurin yi wa wasu mutum biyu fashin kuɗin da ya kai shilin miliyan biyu.

    Kwatankwacin dala 16,000 a kan wani titi da ke Nairobi babban birnin ƙasar.

    Mutanen biyu - waɗanda ma'aikatan hukumar musayar kuɗin kasashen waje ne - sun cire kuɗin ne a wani banki a lokacin da 'yan sandan ke lura da su.

    To sai dai yunƙurin fashin bai yi nasara ba, sakamakon kururuwa da mutanen biyu suka yi.

    Daga baya dai an kama jami'an 'yan sandan huɗu tare da gurfanar da su a gaban kotu domin fuskantar sharia'a.

    View more on twitter
  20. Birtaniya ta ci tarar bankin GT dala miliyan 9.3 saboda gazawa a tsare-tsarensa

    GT Bank

    Hukumar da ke sa ido kan hada-hadar kuɗi ta Birtaniya ta ci tarar bankin GT dala miliyan 9.3 saboda gazawa a tsare-tsarensa na magance matsalar almundahanar kuɗaɗe.

    A wata sanarwa da hukuma ta fitar, ta ce bankin ya gaza a tsarinsa na hana almundahanar kuɗi.

    Kamfanin dillacin labari na Reuters ya ruwaito hukumar na cewa bankin ya kasa ɗaukar matakan da suka dace domin magance tsare-tsaren kare almundahanar kuɗaɗe, duk kuwa da irin gargaɗin da aka sha yi masa.

    “Bankin da kansa ya gano irin tarin matsalolin da gazawar ke haifarwa, haka mu ma hukumarmu, amma duk da haka bankin bai ɗauki matakan da suka dace ba” kamar yadda sanarwar hukumar hada-hadar kuɗin ƙasar ta bayyana.

    Haka kuma hukumar ta ce bankin bai ƙaryata gazawarsa da hukumar ta gano ba, sannan kuma ya amince zai biya tarar.

    A wata sanarwa da bankin ya fitar, ya ce ya sasanta da hukumar hada-hadar kuɗin, ya kuma amince da abin da hukumar ta gano na gazawarsa tsakanin watan Oktoban 2014 zuwa Yulin 2019.

    Sannan kuma ya amince zai biya tarar kamar yadda hukumar ta buƙata.