Masu bibiyarmu nan za mu rufe wannan shafi namu na kai-tseye wanda muka kawo muku yadda aka gudanar da muhawarar 'yanh takarar gwamna a jihar Kano da ke arewa maso yammacin najeriya.
Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu sake dawo wa domin ci gaba da kawo muku sabbin labarai.
Kada kuma ku manta kuna iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin kallon yadda muhawarar ta gudana.
A madadin sauran abokan aiki Abdullahi Bello Diginza ke cewa mu kwana lafiya
DiginzaCopyright: Diginza
Zan tsaya wa Nnamdi Kanu idan gwamnati za ta sake shi - Soludo
Gwamnan jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya Chukwuma Soludo, ya yi kira ga shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da ya saki shugaban ƙungiyar 'yan awaren Biafra ta IPOB Nnamdi Kanu.
Gwamnan ya ce a shirye yake ya tsaya wa Nnamdi Kanu wanda ke hannun jam'ian tsaro na farin kaya a ƙasar, matuƙar gwamnati za ta sake shi.
Mista Soludo ya yi kiran ne a lokacin gangamin yaƙin neman zaɓe a birnin Akwa na jihar, inda ya ce matsalar tsaron da yankin kudu maso gabashin ƙasar ke fuskanta na da alaƙa da manyan jagororin ƙungiyar IPOB.
Dan haka a cewarsa dole ana buƙatar jagororin ƙungiyar a teburin tattaunawar sulhu tsakanin gwamnati da ƙungiyar.
A 'yan kwanakin nan ne dai wata kafar yada labarai a ƙasar ruwaito mai tsawatarwa na majalisar dattawan ƙasar, wato tsohon gwamnan jihar Abia da ke kudu maso gabashin ƙasar Orji Kalu na cewa shi ma zai tsaya wa jagoran 'yan awaren domin a sake shi.
United ta lallasa Man City a Old Trafford
Getty ImagesCopyright: Getty Images
Manchester United doke takwararta Manchester City da ci 2-1 a wasan hammayya da ƙungiyoyin biyu suka buya a filin wasa na Old Trafford.
City ce ta fara cin ƙwallo ta hannun Jack Grealish a ƙoƙarin da ƙungiyar ke yi na rage yawan tazarar maki da ke tsakaninta da Arsenal wadda ke ta ɗaya a kan teburin Premier.
To sai dai haƙar City ba ta cimma ruwa ba, bayan da Bruno Fernandes ya farke ƙwallon ana saura minti 12 a tashi wasan, duk da kasancewar Marcus Rashford a cikin da'irar satar gida.
Minti huɗu bayan hakan ne kuma Marcus Rashford ɗin ya ƙara ta biyu bayan da ya zura ƙwallon da Alejandro Garnacho ya bugo masa.
Da wannan sakamako United ta koma ta uku a kan taburin maki ɗaya tsakaninta da City wadda ke matsayi na biyu, maki biyar tsakaninta da Arsenal ta ɗaya.
Gane Mini Hanya
Hira da Sanata Ibrahim shekarau
Gwamnatin Zamfara ta gano likitocin bogi 199 da ke karɓar albashi
Zamfara govtCopyright: Zamfara govt
Gwamnan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya Muhammad Bello Matawalle ya ce gwamnatin jihar ta gano sunayen likitocin bogi kimanin 199 waɗanda ake biyan albashi a jihar.
Gwamna matawalle na wannan jawabi ne ga taron manema labarai a shalkwatar ƙaramar hukumar Maradun da ke jihar.
A cewar gwamnan yayin da gwamnatin jihar ke biyan likitoci 280 albashi a jihar a duk wata, ta gano cewa likitoci 81 ne kawai ke aiki a jihar.
Gwamnan ya ƙara da cewa tuni ya zanta da ƙungiyar kwadago ta ƙasa domin gano waɗanan, likitoci 199 da suka ƙwashe tsawon lokaci suna karɓar albashi alhalin ba sa yi wa gwamnatin jihar aiki.
Da kuma gano waɗanda ke da hannu a wannan cuwa-cuwa.
Matawalle ya ce an gano waɗannan sunaye ne sakamakon aikin tantance ma'aikata da gwamnatin jihar ke gudanarwa ƙarƙashin ofishin shugaban ma'aikata na jihar.
Shirin Lafiya Zinariya
Shirin Lafiya Zinariya na wannan makon ya yi duba ne a kan ciwon 'Hangun'"
Ci gaba da kawo muku sauran labarai
Yanzu kuma za mu ci gaba da kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sauran sassan duniya.
Ku ci gaba da kasancewa da mu domin sanin halin da duniya ke ciki.
BBC Hausa! Labaran duniya a duk inda kuke!
Kammala muhawara
BBCCopyright: BBC
Masu bin mu a wannan shafi yadda ta kaya kenan a muhawar 'yan takarar gwamna na jihar Kano da BBC Hausa ta shirya.
Amma kar ku manta za ku iya sake kallon wannan muhawa a shafukanmu na BBC Hausa Facebook, da YouTube.
Haka kuma wannan muhawara ita ce farko daga cikin jerin muhawara da BBC Hausa ta shirya yi da 'yan takarar gwamna a wasu jihohin arewacin ƙasar biyar.
Za mu kawo muku muhawararmu ta gaba a daga jihar Kaduna ranar 18/01/2023. Sai ku tara da mu a wannan rana domin kawo muku muhawar tare da 'yan takarar gwamnan jihar ta Kaduna.
Bayan jihar Kaduna kuma sai jihar Katsina, da Bauchi da kuma jihar Sokoto, myna fata za ku kasance tare da mu domin kallon muhawar a duka waɗannan jihohi.
Mun gode
BBCCopyright: BBC
Jawabin kammalawa: Sha'aban Sharada
BBCCopyright: BBC
''Ina kira ga magoya bayanmu da mu yi siyasa ba da gaba ba'', in ji shi
Kuma ''za mu yi aiki da matasa ta hanyar zaƙulo ma'aidan da Kano ke da su''.
daga ƙarshe ya yi alƙwarin yin aiki tare da kowa
Jawabin kammalawa: Nasiru Yusuf Gawuna
''A duba mutumin da ya cancanta a zaɓa'', A yi siyasa cikin lumana, domin kuwa ''yanzu da muka zo nan BBC Hausa ta sauke mu a ɗaki ɗaya kuma duka muka gaisa tare da mutunta junanmu'', dan haka ina kira ga magoya bayanmu da su zauna lafiya''
BBCCopyright: BBC
Jawabin kammalawa: Mohammed sani Abacha
''Ina fatan za a mu yi wa juna da 'yan uwa adalci''
BBCCopyright: BBC
Jawabin kammalawa: Salihu Tanko Yakasai
BBCCopyright: BBC
Nasiru Yusuf Gawuna kan tambayoyin jama'a
Kawar da maganar Rashawa
Tsarkake zukata domin yin abin da ya dace
Gyara tsarin bayar da kwangila
Yin doka domin samar da hukumar masu bukata ta musamman
Inganta ɗakunan gwaje-gwaje
BBCCopyright: BBC
Sha'aban Sharada
Horar da matasa kan fasahar zamani da ICT
Gwanati za ta riƙa wallafa abun da ta samu da abin da ta kashe a duka wata a shafin intanet
Samar da makarantu da inganta waɗanda ake da su ga masu buƙatar lalura da musamman
Salihu Tanko Yakasai kan tambayoyin mutane
Babu maganar 10 fasen a gwamnatinsa
Za a dama da masu buƙatar lalura ta musamman ta hanyar horas da su sana'o'i
BBCCopyright: BBC
Mohammen Abacha kan tambayoyin da aka yi
Bayar da kwangila ga 'yan asalin jihar Kano maimakon 'yan wasu jihohin ko 'yan ƙasashen waje, sannan za mu tabbatar da aikin kwangila ya inganta da ayadda za a yi aiki mai inganci,
Tabbatar da cewa 'yan kwangila sun cika ƙa'ida
Yanzu an zo gabar tambayoyi daga masu sauraro
Yanzu kuma lokacin masu tambayoyi ne waɗanda za su yi tambayoyinsu ga 'yan takarar
BBCCopyright: BBC
Haɓaka kasuwanci: Salihu Tanko Yakasai
Samar da jari ga 'yan kasuwa
'Yan kasuwar Kano su tsaya da kafafunsu, su daina zama dilallai
Inganta wutar lantarki a jihar Kano
Zamanatar da kasuwanci da kasuwannin Kano
Gyara kasuwanni domin tsaftace su daga kwatami
Zamanantar da kasuwar 'yan kaba
Bunƙasa kasuwanci : Sha'aban Sharada
Inganta harkokin samun kudin shiga
bayar da cikakken yancin kudi ka ƙananan hukumomi
Gyara masa'antun chalawa da na Bomfai
Janyo 'yan kasuwa daga ƙasashen waje domin su zo su zuba jari
Samar da ƙananan bankunan bayar da rance domin inganta jihar
Inganta kudin shigar Kano zuwa biliyan 10
BBCCopyright: BBC
Noma da Kiwo: Mohammed Sani Abacha
BBCCopyright: BBC
Samar da ingantaccen iri na zamani
Inganta madatsun ruwan da Kano ke da su domin haɓaka harkar noma
Rahoto kai-tsaye
Daga Abdullahi Bello Diginza
time_stated_uk
Rufewa
Masu bibiyarmu nan za mu rufe wannan shafi namu na kai-tseye wanda muka kawo muku yadda aka gudanar da muhawarar 'yanh takarar gwamna a jihar Kano da ke arewa maso yammacin najeriya.
Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu sake dawo wa domin ci gaba da kawo muku sabbin labarai.
Kada kuma ku manta kuna iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin kallon yadda muhawarar ta gudana.
A madadin sauran abokan aiki Abdullahi Bello Diginza ke cewa mu kwana lafiya
Zan tsaya wa Nnamdi Kanu idan gwamnati za ta sake shi - Soludo
Gwamnan jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya Chukwuma Soludo, ya yi kira ga shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da ya saki shugaban ƙungiyar 'yan awaren Biafra ta IPOB Nnamdi Kanu.
Gwamnan ya ce a shirye yake ya tsaya wa Nnamdi Kanu wanda ke hannun jam'ian tsaro na farin kaya a ƙasar, matuƙar gwamnati za ta sake shi.
Mista Soludo ya yi kiran ne a lokacin gangamin yaƙin neman zaɓe a birnin Akwa na jihar, inda ya ce matsalar tsaron da yankin kudu maso gabashin ƙasar ke fuskanta na da alaƙa da manyan jagororin ƙungiyar IPOB.
Dan haka a cewarsa dole ana buƙatar jagororin ƙungiyar a teburin tattaunawar sulhu tsakanin gwamnati da ƙungiyar.
A 'yan kwanakin nan ne dai wata kafar yada labarai a ƙasar ruwaito mai tsawatarwa na majalisar dattawan ƙasar, wato tsohon gwamnan jihar Abia da ke kudu maso gabashin ƙasar Orji Kalu na cewa shi ma zai tsaya wa jagoran 'yan awaren domin a sake shi.
United ta lallasa Man City a Old Trafford
Manchester United doke takwararta Manchester City da ci 2-1 a wasan hammayya da ƙungiyoyin biyu suka buya a filin wasa na Old Trafford.
City ce ta fara cin ƙwallo ta hannun Jack Grealish a ƙoƙarin da ƙungiyar ke yi na rage yawan tazarar maki da ke tsakaninta da Arsenal wadda ke ta ɗaya a kan teburin Premier.
To sai dai haƙar City ba ta cimma ruwa ba, bayan da Bruno Fernandes ya farke ƙwallon ana saura minti 12 a tashi wasan, duk da kasancewar Marcus Rashford a cikin da'irar satar gida.
Minti huɗu bayan hakan ne kuma Marcus Rashford ɗin ya ƙara ta biyu bayan da ya zura ƙwallon da Alejandro Garnacho ya bugo masa.
Da wannan sakamako United ta koma ta uku a kan taburin maki ɗaya tsakaninta da City wadda ke matsayi na biyu, maki biyar tsakaninta da Arsenal ta ɗaya.
Gane Mini Hanya
Hira da Sanata Ibrahim shekarau
Gwamnatin Zamfara ta gano likitocin bogi 199 da ke karɓar albashi
Gwamnan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya Muhammad Bello Matawalle ya ce gwamnatin jihar ta gano sunayen likitocin bogi kimanin 199 waɗanda ake biyan albashi a jihar.
Gwamna matawalle na wannan jawabi ne ga taron manema labarai a shalkwatar ƙaramar hukumar Maradun da ke jihar.
A cewar gwamnan yayin da gwamnatin jihar ke biyan likitoci 280 albashi a jihar a duk wata, ta gano cewa likitoci 81 ne kawai ke aiki a jihar.
Gwamnan ya ƙara da cewa tuni ya zanta da ƙungiyar kwadago ta ƙasa domin gano waɗanan, likitoci 199 da suka ƙwashe tsawon lokaci suna karɓar albashi alhalin ba sa yi wa gwamnatin jihar aiki.
Da kuma gano waɗanda ke da hannu a wannan cuwa-cuwa.
Matawalle ya ce an gano waɗannan sunaye ne sakamakon aikin tantance ma'aikata da gwamnatin jihar ke gudanarwa ƙarƙashin ofishin shugaban ma'aikata na jihar.
Shirin Lafiya Zinariya
Shirin Lafiya Zinariya na wannan makon ya yi duba ne a kan ciwon 'Hangun'"
Ci gaba da kawo muku sauran labarai
Yanzu kuma za mu ci gaba da kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da ma sauran sassan duniya.
Ku ci gaba da kasancewa da mu domin sanin halin da duniya ke ciki.
BBC Hausa! Labaran duniya a duk inda kuke!
Kammala muhawara
Masu bin mu a wannan shafi yadda ta kaya kenan a muhawar 'yan takarar gwamna na jihar Kano da BBC Hausa ta shirya.
Amma kar ku manta za ku iya sake kallon wannan muhawa a shafukanmu na BBC Hausa Facebook, da YouTube.
Haka kuma wannan muhawara ita ce farko daga cikin jerin muhawara da BBC Hausa ta shirya yi da 'yan takarar gwamna a wasu jihohin arewacin ƙasar biyar.
Za mu kawo muku muhawararmu ta gaba a daga jihar Kaduna ranar 18/01/2023. Sai ku tara da mu a wannan rana domin kawo muku muhawar tare da 'yan takarar gwamnan jihar ta Kaduna.
Bayan jihar Kaduna kuma sai jihar Katsina, da Bauchi da kuma jihar Sokoto, myna fata za ku kasance tare da mu domin kallon muhawar a duka waɗannan jihohi.
Mun gode
Jawabin kammalawa: Sha'aban Sharada
''Ina kira ga magoya bayanmu da mu yi siyasa ba da gaba ba'', in ji shi
Kuma ''za mu yi aiki da matasa ta hanyar zaƙulo ma'aidan da Kano ke da su''.
daga ƙarshe ya yi alƙwarin yin aiki tare da kowa
Jawabin kammalawa: Nasiru Yusuf Gawuna
''A duba mutumin da ya cancanta a zaɓa'', A yi siyasa cikin lumana, domin kuwa ''yanzu da muka zo nan BBC Hausa ta sauke mu a ɗaki ɗaya kuma duka muka gaisa tare da mutunta junanmu'', dan haka ina kira ga magoya bayanmu da su zauna lafiya''
Jawabin kammalawa: Mohammed sani Abacha
''Ina fatan za a mu yi wa juna da 'yan uwa adalci''
Jawabin kammalawa: Salihu Tanko Yakasai
Nasiru Yusuf Gawuna kan tambayoyin jama'a
Kawar da maganar Rashawa
Tsarkake zukata domin yin abin da ya dace
Gyara tsarin bayar da kwangila
Yin doka domin samar da hukumar masu bukata ta musamman
Inganta ɗakunan gwaje-gwaje
Sha'aban Sharada
Horar da matasa kan fasahar zamani da ICT
Gwanati za ta riƙa wallafa abun da ta samu da abin da ta kashe a duka wata a shafin intanet
Samar da makarantu da inganta waɗanda ake da su ga masu buƙatar lalura da musamman
Salihu Tanko Yakasai kan tambayoyin mutane
Babu maganar 10 fasen a gwamnatinsa
Za a dama da masu buƙatar lalura ta musamman ta hanyar horas da su sana'o'i
Mohammen Abacha kan tambayoyin da aka yi
Bayar da kwangila ga 'yan asalin jihar Kano maimakon 'yan wasu jihohin ko 'yan ƙasashen waje, sannan za mu tabbatar da aikin kwangila ya inganta da ayadda za a yi aiki mai inganci,
Tabbatar da cewa 'yan kwangila sun cika ƙa'ida
Yanzu an zo gabar tambayoyi daga masu sauraro
Yanzu kuma lokacin masu tambayoyi ne waɗanda za su yi tambayoyinsu ga 'yan takarar
Haɓaka kasuwanci: Salihu Tanko Yakasai
Samar da jari ga 'yan kasuwa
'Yan kasuwar Kano su tsaya da kafafunsu, su daina zama dilallai
Inganta wutar lantarki a jihar Kano
Zamanatar da kasuwanci da kasuwannin Kano
Gyara kasuwanni domin tsaftace su daga kwatami
Zamanantar da kasuwar 'yan kaba
Bunƙasa kasuwanci : Sha'aban Sharada
Inganta harkokin samun kudin shiga
bayar da cikakken yancin kudi ka ƙananan hukumomi
Gyara masa'antun chalawa da na Bomfai
Janyo 'yan kasuwa daga ƙasashen waje domin su zo su zuba jari
Samar da ƙananan bankunan bayar da rance domin inganta jihar
Inganta kudin shigar Kano zuwa biliyan 10
Noma da Kiwo: Mohammed Sani Abacha
Samar da ingantaccen iri na zamani
Inganta madatsun ruwan da Kano ke da su domin haɓaka harkar noma
Wadata jihar da takin zamani da magungunan ƙwari