Got a TV Licence?

You need one to watch live TV on any channel or device, and BBC programmes on iPlayer. It’s the law.

Find out more
I don’t have a TV Licence.

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

time_stated_uk

  1. 'Yan sanda sun kama mutum biyar bisa zargin cire sassan jikin gawarwaki

    'Yan sanda

    Rundunar 'yan sandan jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya ta ce ta kama wasu mutum biyar da take zargi da kasancewa 'yan ƙungiyar asiri da suka yi shura wajen tono kaburbura domin cire sassan jikin gawarwaki don yin tsafi.

    Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan jihar Abimbola Oyeyemi ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a birnin Abeokuta.

    Oyeyemi ya ce an kama mutanen ne bayan da suka samu bayan sirri cewa gungun mutanen za su fita neman sassan jikin mutane a cikin Ososa.

    Inda ya ce nan take jami'an 'yan sanda ƙarƙashin jagorancin Baturen 'yan sandan Odogbolu Godwin Idehai suka dirar musu tare da kama mutum biyar daga cikinsu.

    “Bayan da aka fara tuhumar ne kuma mutanen suka bayyana wa 'yan sanda cewa sun daɗe suna aikata wannan laifi, inda suke tona kaburbura domin cire sassan jikin gawarwaki,'' in ji Oyeyemi.

    “Sun ce sukan sayar da sassan jikin gawarwakin ga wasu mutane da ke amfani da su wajen yin tsafi domin samun kuɗi'', in ji shi.

  2. 'Yan sanda sun sha alwashin kama maharan Kaduna

    Rundunar 'yan sandan jihar Kaduna ta sha alwashin kama waɗanda suka kai hari tare da kisan mutum 17 a ƙauyen Unguwan Wakili da ke cikin ƙaramar hukumar Zango Kataf a jihar.

    Yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar Muhammad Jalige, cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce ɗaukar matakan gaggawa da haɗin gwiwwar jami'an tsaro suka ɗauka ne ya hana 'yan bindigar ci gaba munanan hare-haren.

    Jagile ya tabbatar da cewa jami'an tsaro na aiki, domin kwantar da hankali a yankin, tare alƙawarta kamo mutanen da suka ƙaddamar da hare-haren domin su fuskanci hukunci.

    Da safiyar ranar Lahadi ne dai rahotonni suka bayyana samun gawar mutum 10 a ƙauyen Unguwan Wakili da ke cikin ƙaramar hukumar Zango Kataf, bayan da wasu 'yan bindiga suka kai wa ƙauyen hare.

    A wata sanarwar da hukumomin ƙaramar hukumar suka fitar sun bayyana sanya dokar hana fita ta tsawon sa'o'i 24 a ƙauyukan Ungwan Juju da Mabuhu da Ungwan Wakili da kuma garin Zango.

  3. NDLEA ta kama basaraken gargajiya da laifin safarar ƙwaya

    Jami'an NDLEA

    Hukumar da ke Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya NDLEA ta ce jami'antsa sun kama wani Basaraken gargajiya da tubabben ɗan Boko Haram da wasu mutum 35 bisa laifin safarar muggan ƙwayoyi.

    A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta Twitter mai ɗauke da sa hannun jami'in hulda da jama'a na hukumar Femi Babafemi, ta ce ta samu nasarar kama muggan ƙayoyin a cikin na'urar daskarar da abubuwa ta 'firinji' da kuma tukwanen gas a filin jirgin sama na Legas da ke kudu maso yammacin ƙasar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa jami'an hukumar sun kuma lalata gonakin da ake noma tabar wiwi da girmansu ya kai hekta 39.8 a jihohin Edo da Ondo.

    Basaraken gargajiyar mai suna Baale Akinola Adebayo - sarkin Kajola, garin da ke kan iyakar jihohin Edo da Ondo - na daga cikin mutum 27 da hukumar ta ce ta kama da laifin safarar ƙwayoyin da nauyinsu ya kai tan 2.2 a faɗin jihohin ƙasar 12 cikin makon da ya gabata.

    Haka kuma hukumar ta ce ta kama Alayi Modu - wanda ya ƙwashe shekara 15 yana cikin ƙungiyar Boko Haram - kafin ya miƙa wuya a shekarar 2021.

    Shugaban hukumar Janar Buba Marwa mai ritaya ya jinjina wa jami'an hukumar a jihohin ƙasar 12 bisa namijin ƙoƙarin da ya ce sun yi wajen kamen miyagun ƙwayoyin.

    View more on twitter
  4. 'Yan tawayen M23 sun kashe mutum 17 a gabashin DR Kongo

    'Yan tawaye

    'Yan tawayen M23 a gabashin Jamhuriyar Dimkraɗiyyar Kongo sun kashe kutum 17, kisan gilla na biyu cikin ƙasa da mako guda.

    Rahotonni sun ce 'yan tawayen sun cinna wa gine-gine wuta a lokacin harin da suka kai da asubahi a garin Kirindera da ke lardin arewacin Kivu.

    A ranar Larabar da ta gabata mutum 45 aka kashe lokacin wani samamen da 'yan tawayen - waɗanda ake alaƙantawa da ƙungiyar ISIS - suka kai wasu ƙauyuka biyu.

    Ana ta ƙoƙari tattaunawa da ɓangarorin biyu domin samun zaman lafiya a yankin, to amma ƙasashe na ci gaba da tura dakaru domin wanzar da zaman lafiya a gabashin Kongon.

    Sojojin Uganda sun kwashe fiye da shekara guda a yankin na arewacin lardin Kivu domin yaƙar 'yan tawayen, ba tare da samun nasara ba. A wannan makon kaɗai 'yan tawayen sun kashe gomman fararen hula a ƙauyuka uku.

    Ana ci gaba da nuna damuwa da ayyukan 'yan tawayen na M23 waɗanda ake yawan alaƙantawa da samun goyon bayan Rwanda.

    A yanzu Angola na shirin tura dakaru zuwa lardin arewacin Kivu domin taimaka wa sojojin gwamnati.

    Tuni dai dama dakarun Kenya da na Burundi ke lardin, tare da fatn yi wa 'yan tawayen taron dangi.

  5. Kamfanin mai na Saudiyya ya samu riba mafi yawa ta fiye da dala biliyan 161

    Kamfanin mai

    Kamfanin mai na ƙasar Saudiyya 'Aramco' ya bayyana samun riba mafi yawa ta dala biliyan 161.1 a shekarar 2022, sakamakon tashin farashin makamashi a faɗin duniya.

    Ribar da kamfanin ya samu a shekarar da ta gabata ya kai ƙarin kashi 46 cikin ɗari na abin da kamfanin ya samu a shekarar da ta gabata.

    Ribar ita ce ta baya-bayan nan da wani kamfanin makamashi ya bayyana samu, bayan tashin farashin makamashi da ya shafi duniya sakamakon yaƙin Ukraine.

    Kamfanin mai na Amurka ExxonMobil ne na biyu inda ya samu ribar dala biliyan 55.7, sai kuma kuma kamfanin man Birtaniya na Shell da ya samu ribar dala biliyan 39.9

    Kamfanin na 'Aramco' ya kuma bayyana ware ribar dala biliyan 19.5 da zai rabar wa masu hannayen jari a kamfanin cikin watanni ukun farko na wannan shakera.

    Mafi yawan kuɗin da kamfanin zai biya abokan hulɗar tasa, za su tafi asusun gwamnatin ƙasar ne wadda ta mallaki kusan kashi 95 cikin ɗari na hannayen jarin kamfanin.

    A yanzu ana sayar da gangar ɗanyen man fetur kusan dala 82, bayan da a watan Maris ɗin bara ya kai kusan dala 120 bayan mamayar da Rasha ta yi wa Ukraine.

  6. Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu

    Video content

    Video caption: Latsa lasifikar da ke sama domin sauraron shirin
  7. 'Yan sanda sun kuɓutar da mutum 14 bayan kwana 68 a hannun 'yan bindiga

    Mutan da aka kuɓutar

    Rundunar 'yan sandan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ce ta samu nasarar lalata dabar 'yan bindiga ta ɗaya daga cikin fitattun 'yan bindigar da suka addabi jihar mai suna Dogo Sule, a kusa da dajin Munhaye.

    A wata sanarwa - da rundunar 'yan sandan jihar ta fitar ta hannun jami'ain huld da jama'a na rundunar SP Mohammed Shehu - ta ce wani samamen haɗin gwiwwa da ta ƙaddamar tare da rundunar 'yan sa kai ne ya kai ga nasarar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa sakamakon samamen an kuɓutar da mutum 14, da suka haɗar da maza biyu, da mata bakwai da kuma ƙananan yara biyar 'yan ƙasa da shekara biyu.

    Yayin da suke yi wa 'yan sanda bayani, mutanen sun ce tun a ranar ɗaya ga watan Janairu ne 'yan bindigar suka sace su daga ƙauyukan Anguwar Mangoro da Gidan Maidawa a yankin ƙaramar hukumar Gusau, inda suka ci gaba da ajiye su a sansanin tsawon kwanaki 68.

    Mutanen waɗanda ke cikin halin tausayi, an kai su asibiti domin ba su kulawar da ta dace kafin a sada su da iyalansu, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

    Sanarwar ta kuma ambato kwamishinan 'yan sandan jihar CP Kolo Yusuf na taya mutanen murnar kuɓuta daga hannun miyagun, tare da sake jaddada ƙudurin rundunar na tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin al'ummar jihar.

    Mutanen da aka kuɓutar
  8. Mauritaniya ta kashe masu iƙirarin jihadin da suka tsere daga gidan yari

    Masu iƙirarin Jihadi

    Gwamnatin ƙasar Mauritaniya ta ce jami'an tsaronta sun kashe masu iƙirarin jihadi uku daga cikin huɗun da suka tsere daga wani gidan yarin ƙasar cikin makon da ya gabata.

    Gwamnatin ta ce an kashe fursunonin uku ne tare da sake kama ɗaya daga cikinsu a wata arangama da jami'an tsaro a arewacin ƙasar, lamarin da ya kai ga kisan jami'in ɗan sanda ɗaya.

    Rahotonni sun ce bayan da suka tsere daga gidan yarin da ke Nouakchott babban birnin ƙasar, masu iƙirarin jihadin sun shafe ɗaruruwan kilomitoci suna keta sahara a yankin arewacin ƙasar.

    Jami'an tsaro sun ce sun yi musayar wuta da masu iƙirarin jihadin a yankin Adrar mai tsaunuka.

    Ɗaya daga cikin waɗanda aka kashen mai suna Saleck Ould Cheikh Mohamedou na aiki ne da ƙungiyar Al Qaeda da ke yankin arewacin Afirka.

    A shekarar 2015 ya taɓa tserewa daga wani gidan yari bayan da aka yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai bisa samunsa da laifin kitsa shirin da bai yi nasara ba na kashe tsohon shugaban ƙasar.

    Haka kuma an zarge shi da shirya harin da ya yi sanadiyyar kashe masu yawon buɗe huɗu 'yan asalin Faransa.

  9. Amsoshin Takardunku

    Shirin namu na wannan mako wanda Raliya Zubairu ta gabatar da amsa tambayar Nafisa Lawal daga jihar Katsina ta aiko mana domin neman ƙarin bayani kan cutar sankarar hanji.

    Ta kuma miƙa tambayar ga Dakta Hannatu Ayuba ƙwararriyar likitan kansa a Abuja

    Video content

    Video caption: Latsa lasifikar da ke sama domin sauraron shirin
  10. An gudanar da zanga-zanga mafi girma a tarihin Isra'ila

    Masu zanga-zanga

    Dubban ɗaruruwan 'yan Isra'ila ne suka gudanar da zanga-zangar adawa da shirin gwamnatin ƙasar na yin sauye-sauye a ɓangaren shari'ar ƙasar, zanga-zangar da masu shirya ta suka kira mafi girma a tarihin ƙasar.

    Firaministan ƙasar Benjamin Netanyahu ya ce sauye-sauyen -waɗanda za su rage ƙarfin ikon da kotunan ƙasar ke da shi - za su taimaka wajen daidaita iko tsakanin ɓangarorin gwamnati.

    Matakin da 'yan adawa ke kallo a matsayin barazana ga dimokraɗiyya.

    A ɗaya daga cikin zanga-zangar da ya jagoranta shugaban adawa na ƙasar Yair Lapid ya ce wannan babbar 'barazana ce ga ƙasar''.

    Kafofin yaɗa labaran Isra'ila sun ce mutum 500,000 suka fito kan tituna domin gudanar da zanga-zangar da suka kira mafi girma a tarihin ƙasar.

    A Tel Aviv babban birnin ƙasar kimanin mutum 200,000 ne suka gudanar da zanga-zangar riƙe da tutar ƙasar.

    Tamir Guytsabry na ɗaya daga cikin mutanen da suka gudanar da zanga-zangar a birnin, ya kuma shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa ''wannan ba gyara ɓangaren shari'a ba ne, juyin-juya-hali ne da zai mayar da Isra'ila kan takarfin mulkin kama-karya, ni kuma ina son Isra'ila ta kasance kan tsarin dimokraɗiyya ko don 'ya'yana''.

    Masu zanga-zangar sun yi ta tafa wa babban jami'an 'yan sandan birnin yayin da ya ratso ta cikin masu zanga-zangar.

    Tun da farko dai gwamnatin Netanyahu ta buƙaci tuɓe babban jami'in 'yan sandan, to sai dai babban alƙalin ƙasar ya hana yiyuwar hakan.

  11. 'Yan bindiga sun sace mutum tara a Abuja

    'Yan bindiga

    'Yan bindiga sun kai hari tare da sace wasu mutum tara a rukunin gidaje na 'Grow Homes' da ke unguwar Kubwa a wajen Abuja babban birnin Tarayyar Najeriya

    Rahotonni sun ce 'yan bindigar su kimanin 20 sun yi wa rukunin gidajen dirar mikiya ranar Juma'a da daddare.

    Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan birnin tarayya SP Josephine Adeh ta tabbatar wa da BBC faruwar lamarin, tana mai cewa bayan da suka samu kiran waya daga yankin, nan take suka tura jami'an 'yan sanda domin fatattakar 'yan bindigar.

    To sai dai ta ce kafin zuwan jami'an tsaron 'yan bindigar sun gudu da mutanen da suka sace zuwa cikin daji.

    Ta kuma ƙara da cewa 'yan sanda na ƙoƙari wajen ganin sun kuɓutar da mutanen da aka sacen.

  12. Jam'iyyar LP ta yi barazanar gudanar da zanga-zanga a ofisoshin INEC

    LP

    Jam'iyyar Labour a Najeriya ta yi barazanar gudanar da zanga-zanga a ofisoshin hukumar zaɓe da ke faɗin ƙasar kan ƙin ba ta damar duba na'urorin BVAS da aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasar da su ranar 25 ga watan Fabrairu.

    Dan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar Peter Obi ya nemi kotu da ta hana INEC sake saita na'ororin BVAS da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasar.

    To amma kotun ta bai wa INEC damar saita na'urorin tare da bai wa Obi damar duba kayayyakin da aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasar da su.

    To sai dai kwanaki bayan hukuncin kotun mai magana da yawun kwamityin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam'iyyar Dr Yunusa Tanko ya zargi hukumar zaɓen da ƙin bin umarnin kotu.

    “Yayin da muke magana a yanzu INEC ta zaɓi bin umarnin da kotu ta ba ta na sake saita na'urorin BVAS, aikin da take cikin yi yanzu haka, sannan kuma ta ƙi bin umarnin damar da kotun ta ba mu na duba kayyakin da aka gudanar da aikin zaɓen,'' kamar yadda ya bayyana a sanarwar da ya fitar.

    “Dan haka za mu kira magoya bayanmu da su gudanar da zanga-zangar lumana wadda doka ta amince da ita, a ofisoshin hukumar zaɓe da ke faɗin ƙasar nan''.

    Ya ƙara da cewa abin da ya sa ba za su gudanar da zanga-zangar a kan titunan ƙasar ba, shi ne ba sa so a ɗauki zanga-zangar tasu a matsayin tayar da hankali.

  13. An tsinci gawar mutum 10 a Kaduna bayan 'yan bindiga sun kai hari wani ƙauye

    'Yan bindiga

    An samu akalla gawar mutum 10 a ƙauyen Unguwar Wakili da ke cikin ƙaramar hukumar Zango Kataf a jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya, bayan da wasu 'yan bindiga suka kai wa ƙauyen hare.

    A wata sanarwar da hukumomin ƙaramar hukumar suka fitar sun bayyana sanya dokar hana fita ta tsawon sa'o'i 24 a ƙauyukan Ungwan Juju da Mabuhu da Ungwan Wakili da kuma garin Zango.

    Sanarwar da mai taimaka wa shugaban ƙaramar hukumar kan harkokin yaɗa labarai Yabo Chris Ephraim, ya sanya wa hannu ta ce an sanya dokar hana fitar ne domin bai wa jami'an tsaro damar maido da zaman lafiya a yankunan.

    Jihar Kaduna dai na ɗaya daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da hare-haren 'yan bindiga.

  14. Tinubu zai gana da zaɓaɓɓun 'yan majalisa kan shugabancin majalisun tarayya

    ASIWAJU BOLA TINUBU

    Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta gayyaci zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu, tare da mataimakinsa Kashim Shettima, da sauran zaɓaɓɓun sanatoci na 'yan majalisar wakilai na jam'iyyar zuwa wata ganawa ta musamman.

    An tsara gudanar da ganawar ranar Litinin a fadar gwamnati da ke Abuja babban birnin ƙasar.

    Rahotonni na cewa an tsara ganawar ne domin tattauna batun shugabancin majalisun dokokin ƙasar biyu da yadda za a rarraba muƙaman majalisun zuwa shiyyoyin ƙasar daban-daban.

    Gayyatar ganawa da zaɓaɓɓun wakilan - wadda sakataren jam'iyyar na ƙasa, Iyiola Omisore ya sanya wa hannu aka kuma wallafa a shafin jam'iyyar na Twitter - ta bayyan cewa za a yi ganawar ne ranar Litinin 13 ga watan Maris da misalin ƙarfe 12:00 na rana.

    Jam'iyyar ta kuma buƙaci duka zaɓaɓɓun wakilan su hallara tare da takardun shaidar cin zaɓe da hukumar zaɓen ƙasar ta ba su.

    Ganawar na zuwa ne bayan da tuni wasu 'yan majalisun suka fara bayyana sha'awarsu ta zama shugabannin majalisun dokokin ƙasar biyu.

    Samun haɗin kan shugabancin majalisun biyu dai na da matuƙar tasiri wajen gudanar da ayyuka a ɓangaren shugaban ƙasa.

  15. Assalamu alaikum

    Masu bin mu a wannan shafi barkanmu da hutun ƙarshen mako, Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ke a daidai wannan lokaci.

    Ku ci gaba da kasancewa da mu domin sanin irin wainar da ake toyawa musamman a Najeriya da makwabtan ƙasashe.

    Kar ku manta da shafukanmu na sada zumunta domin tofa albarkacin bakinku.

    Mu je zuwa ...