Got a TV Licence?

You need one to watch live TV on any channel or device, and BBC programmes on iPlayer. It’s the law.

Find out more
I don’t have a TV Licence.

Rahoto kai-tsaye

Daga Awwal Ahmad Janyau da Umar Mikail

time_stated_uk

  1. Mun zo ƙarshen rahotannin

    Nan muke rufe wannan shafi. Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu.

    Umar Mikail ne ke muku fatan alheri.

  2. Sojojin Najeriya sun ceto ƙarin ɗaliban sakandare a Jihar Kebbi

    FGC Birnin Yauri

    Rundunar sojan Najeriya ta ce ta ceto ƙarin mutum huɗu daga cikin malamai da ɗaliban sakandaren garin Birnin Yawuri da 'yan bindiga suka sace a JIhar Kebbi da ke arewacin ƙasar.

    Wata sanarwa daga rundunar ta ce dakarunta na Operation Hadarin Daji ne tare da tamakon sojan sama suka ceto malami ɗaya da ɗalibai uku.

    Sojojin sun kashe ɗan fashi ɗaya yayin yunƙurin, a cewar sanarwar da Birgediya Onyema Nwachukwu ya fitar ranar Lahadi.

    Ya ce an tura ƙarin sojoji "domin kewaye dajin da zummar hana 'yan fashin sakat".

    A ranar Juma'a ne sojojin suka fara ceto malamai biyu da ɗalibai biyar bayan fafatawa da 'yan fashin, inda ɗaliba ɗaya ta rasa ranta.

    Da tsakar ranar Alhamis ne ƴan bindigar suka kutsa makarantar sakandare ta FGC Birnin Yauri tare da sace ɗaliban.

  3. 'Yan sandan Abuja sun kama matashi da zargin kashe mace, sun kashe ɗan fashi

    'Yan sandan Najeriya

    'Yan sanda a Abuja, babban birnin Najeriya, sun kama wani da ake zargi da kashe wata mata a Kasuwa-Dere da ke yankin Gwagwalada.

    A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar, ASP Yusuf Mariam, ya fitar, jami'an tsaron sun kama matashin ɗan shekara 20 mai suna Danladi Abubakar a ranar Alhamis, 17 ga watan Yuni.

    An kama shi ne bisa zargin kashe wata mata da har yanzu ba a tantance ko wace ce ba.

    Matashin wanda wani wanda aka taba zalinta ya shaida, ya amsa cewa yana cikin wata ƙungiya da ke ƙwace wa mutane wayoyin salula a yankin na Gwagwalada.

    Daga cikin abubuwan da aka same shi da su akwai wuƙa da ake zargin da ita ya kashe matar da kuma waya samfurin Tecno mallakar matar.

    A gefe guda kuma, 'yan sandan sun katse hanzarin wasu 'yan fashi a yankin Kubwa na Abujar, waɗanda suka yi yunƙurin kai wa wani otel hari ranar Juma'a.

    Jami'an sun kashe ɗaya daga cikin maharan sakamakon mummunan raunin da ya ji a musayar wutar da suka yi da 'yan sanda, a cewar sanarwar.

  4. An tsinci gawar sojan Belgium da ya yi wa masallaci barazana

    Hukumomi a Belgium sun ce gawar da aka tsinta a dajin Woodland ta sojannan ne mai tsatstsauran ra'ayi da ake nema ruwa a jallo.

    Jurgen Conings ya ɓata a watan da ya wuce dauke da manyan makamai tare da shi.

    Kafin batansa ya yi barazana ga wani masallaci da kuma wani likita da ke jagorantar yaƙi da cutar korona a Belgium.

    Binciken farko-farko da aka gudanar ya nuna cewa shi da kansa ya kashe kansa.

    Masana sun ce lamarin ya nuna cewa akwai masu tsattsauran ra'ayi a cikin dakarun gwamnatin Belgium.

  5. Ƙungiyar ASUU ta yi barazanar sake shiga yajin aiki

    ASUU

    Ƙungiyar malaman jami'a a Najeriya ta Academic Staff Union of Universities (ASUU) ta yi barazanar sake tsunduma yajin aiki idan ba a biya albashin mambobinta 1,000 ba na wata 13 a faɗin ƙasar.

    Dr. Lazarus Maigoro shugaban ƙungiyar na reshen Jami'ar Jos wanda ya sanar da gargaɗin, ya ce gwamnatin tarayya ta riƙe wasu alawus na malaman jami'ar.

    Ya zargi Babban Akanta na Ƙasa Ahmed Idris da hana malaman albashinsu duk da cewa gwamnati da ASUU sun cimma yarjejeniya game da biyan bashin albashin da suka biyo sakamakon yajin aikin da suka yi na baya-bayan nan.

    Kazalika NAN ya ruwaito shugaban yana zargin cewa ana yi wa malaman barazanar cewa ko dai su bari a saka su cikin tsarin biyan albashi na Integrated Payroll and Personnel Information System (IPPIS) ko kuma a riƙe albashin nasu.

    "Da yawa daga cikin abokan aikinmu a Jami'ar Jos ba a biya su albashi ba tun daga Fabarairun 2020, na kasa gane ta yadda za su je wajen aiki," a cewarsa.

    "Muna fatan duk matakin da ƙungiya ta ɗauka 'yan Najeriya ba za su kalle shi da wata manufa ba, musamman ganin yadda gwamnati da mutanen gari suka yi shuru game da karya dokar yarjejeniyarmu ta 2020 MoA."

    Yajin aiki na baya-bayan nan da ASUU ta yi ya sa ɗliban jami'a sun shafe kusan wata tara a gida ba tare da zuwa makaranta ba.

  6. Wane ne Ebrahim Raisi zaɓaɓɓen shugaban Iran?

    Iran

    Ebrahim Raisi mai tsattsauran ra'ayi kuma na hannun damar babban jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei ya lashe zaben Iran da aka yi makon da ya gabata.

    Raisi mai shekaru 60 ya gabatar da kansa a matsayin wanda ya fi cancanta ya yaƙi cin hanci da rashawa ya kuma warware matsalar tattalin arziki da Iran ta sami kanta a ƙarƙashin shugaba Hassan Rouhani mai barin gado.

    Shine babban jojin Iran, wanda yan ƙasar da sauran masu rajin kare haƙƙin bil-adama ke nuna wa ɗan yatsa kan rawar da ya taka wurin kisan fursunonin siyasa a shekarun 1980.

    An haifi Ebrahim Raisi a shekarar 1960 a garin Mashhad, gari na biyu mafi girma a Iran da ke da babban markazin mabiya Shi'a.

    Mahaifinsa wanda shima malami ne ya mutu a lokacin Raisi na da shekaru biyar da haihuwa.

    Karanta cikakken tarihinsa a nan:

  7. 'Yan sandan Jihar Benue sun kashe 'yan fashi 14

    'Yan sandan Najeriya

    Rundunar 'yan sandan Jihar Benue a tsakiyar Najeriya ta ce ta kashe 'yan fashi 14 yayin wata fafatawa da su bayan sun kai hari ofishin 'yan sandan da ke Kastina-Ala.

    Cikin wata sanarwa, kakakin 'yan sandan jihar, DSP Catherine Anene, ta ce 'yan bindigar masu yawan gaske sun yi yunƙurin ceto abokansu da ake tsare da su a ofishin a safiyar Lahadi.

    "A ranar 19 ga watan Yuni (Asabar) aka kama 'yan fashi biyar aka tsare su a Babban Ofishin 'yan Sanda na Kastina-Ala domin aiwatar da bincike," a cewarta cikin wata sanarwa da Daily Trust ta ruwaito.

    "A ranar Lahadi, 20 ga wata da misalin ƙarfe 1:30 na dare, 'yan fashi fiye da 50 suka far wa ofishin 'yan sanda don su ceto abokansu.

    "An kashe 14 daga cikinsu yayin musayar wuta yayin da wasu da yawa suka tsere da raunukan harbin bindiga."

    Ta ƙara da cewa jami'an tsaro na ci gaba da neman miyagun, tana mai shawartar mazauna Kastina-Ala da su kwantar da hankalinsu.

  8. Iran ta ce an kusa farfaɗo da yarjejeniyar nukiliyarta

    Iran

    Babban mai shiga tsakani na nukiliyar Iran, ya ce Tehran da manyan kasashen duniya shida sun kusa cimma matsaya kan farfado da yarjejeniyar nukiliya ta 2015.

    Bayan tattaunawar da Iran ta yi da wakilan manyan ƙasashen a Vienna ranar Lahadi, Abbas Araqchi ya ce yana fatan za su ci gaba da tattaunawa bayan sabon shugaban Iran da aka zaɓa Ebrahim Raisi ya karɓi ragamar shugabanci a Agusta.

    Sai dai kuma Araqchi ya bayyana cewa akwai ƙalubale kuma ba zai kasance mai sauki ba.

    Yarjejeniyar nukiliya ta 2015 ta dage takunkumi kan Iran a madadin taƙaita ayyukanta na makamashi wanda ya haɗa da bunƙasa makamashin uranium wanda zai kai ta mallaki makaman nukiliya.

  9. Al'adar ci-rani ga ƴan Nijar

    Shirin ci rani a jihar Tawa ta Jumhuriyar Nijar kashi biyar tare da Abdussalam Ibrahim Ahmed.

    Video content

    Video caption: Al'adar ci-rani ga ƴan Nijar
  10. China ta yi wa ƴan ƙasarta biliyan ɗaya allurar korona

    China

    Hukumomin China sun ce an yi wa mutum sama da biliyan ɗaya allurar rigakafin korona – fiye da kashi ɗaya bisa uku na rigakafin da aka yi wa al’ummar duniya.

    An fara aikin rigakafi sannu a hankali bayan da hukumomi suka yi nasarar daƙile masu dauke da kwayar cutar korona.

    Amma tukuicin ƙwai da ake bayar wa domin ƙarfafa gwiwar ƴan ƙasar ga rigakafin da kuma fargaba kan ɓarkewar wani nau’in cutar Delta ya sa aikin rigakafin na ƙara sauri.

    Hukumomin China na fatan yi wa kashi 40 na yawan al’ummar ƙasar zuwa watan Yuli.

    Ana yi wa ƴan China rigakafin da aka samar ne a ƙasar da suka haɗa da Sinopharm da Sinovac da ake dukansu ake yi wa mutum sau biyu.

  11. Saudiyya ta kakkaɓo jiragen Houthi 17 da ke shirin kai mata hari

    Saudiyya ta harbo jiragen yaƙin mayaƙan Houthi marasa matuƙi guda 17 da ke shirin kai mata hari, kamar yadda kafofin yaɗa labaran ƙasar suka ruwaito.

    Daga cikin jiragen har da wanda ya nufi birnin Makkah da nufin kai hari, a cewar rahotannin.

    Kafofin yaɗa labaran gwamnatin Saudiyya sun ce jirage 17 aka harbo cikin sa’a 24.

    Kafar Al Arabiya ta ce duka an harbo jiragen na Houthi ne a samaniyar Yemen kafin su ratso cikin Saudiyya.

    Saudiyya
  12. Shirin Amsoshin Takardunku

    Shirin Amsoshin Takardunkun na wannan mako da Raliya Zubairu ta gabatar ya amsa tambayoyi ne guda biyu. Tarihin tsohon shugaban Zambia na farko Kenneth Kaunda da tarihin gasar cin kofin kwallon kafa ta nahiyar Turai.

    Video content

    Video caption: Amsoshin Takardunku: Tarihin tsohon shugaban Zambia Kenneth Kaunda
  13. SERAP ta kai ƙarar Lai Mohammed kan hana wa kafofin yaɗa labarai amfani da Twitter

    Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci da tabbatar da adalci a Najeriya ta ce ta shigar da ƙara kotu domin ƙalubalantar gwamnatin Buhari kan umarnin hana wa kafafen yaɗa labarai amfani da shafin Twitter.

    A cikin sanarwar daƙungiyar ta fitar ta ce “mun kai ƙarar gwamnatin Buhari da Mista Lai Mohammed kan umarnin ba kafofin yaɗa labarai na talbijin da rediyo su daina amfani da Twitter kuma su goge shafinsu.

    Kungiyar ta ce ta shigar da ƙarar ne a wata Babbar Kotun da ke Abuja, inda ta ke neman kotun ta hana gwamnatin tarayya da hukumar kula da kafofin yaɗa labarai NBC damar kula da ayyukan kafofin sada zumunta na intanet.

    Serap
  14. Taliban ta ce bin tsarin Musulunci ne kawai zai kawo karshen rikicin Afghanistan

    Yayin da ake samun ƙaruwar rikici a Afghanistan, mataimakin shugaban Taliban ya ce za su ci gaba da mutunta tattaunawar zaman lafiya.

    Sai dai kuma Mullah Abdul Ghani Baradar ya bayyana abin da ya kira "bin tsarin Musulunci” ne kawai hanyar da za ta kawo karshen rikicin ƙasar da tabbatar da ƴancin mata da tsiraru.

    Ya yi wannan furuci ne yayin da ake nuna damuwa game da tattaunawar zaman lafiya a Qatar tsakanin mayakan da gwamnatin Afghanistan.

    Taliban ta ci gaba da kai wa gwamnatin Afghanistan hare-hare, yayin da Amurka ke shirin janye sauran dakarunta zuwa watan Satumba.

    Masu sharhi sun ce yawancin ƴan Afghanistan suna fargabar koma wa ga tsattsauran ra'ayi na mulkin Taliban na shekarun 1990 da zarar sojojin ƙasashen waje sun fice ƙasar.

  15. Gwamnan Kebbi ya kira gayyar shiga daji domin ceto ɗaliban Yauri

    Gwamnan Kebbi

    Gwamnan Kebbi Atiku Bagudu ya ce zai shiga daji domin ceto ɗaliban makarantar garin Yauri da ƴan bindiga suka sace.

    Gwamnan ya yi wannan alwashin ne gaban mafarautan jihar Kebbi inda ya ce“Na kira gayya kuma za mu shiga daji.”

    Ya kuma faɗa wa mafarautan cewa su tafi su shirya kafin ya yi magana da shugabannin jami’an tsaro. Ya ce an zaɓe su ne ba don su yi zauna a ofis ba,

    “Dama Kur’ani aka ba mu mun ka yi rantsuwa kuma ba mu yi rantsuwa ba don mu zauna a ofis ba,” in ji shi.

    A ranar Alhamis ne ƴan bindigar suka kutsa Kwalejin Yawuri suka sace ɗalibai da dama.

    Jami’an tsaro sun yi nasarar ceto wasu daga cikin ɗaliban, tare da kashe ƴan bindiga da dama.

    Rahotanni sun ce an yi gumurzu sosai tsakanin jami’an tsaro da ɓarayin dajin a ƙaramar hukumar Sakaba ta jihar Kebbi.

  16. Ana bikin ranar ƴan gudun hijira ta duniya

    Yau 20 ga watan Yuni ranar masu gudun-hijira, wadda majalisar dinkin duniya ta kebe don nazarin halin da suke ciki, da hanyoyin inganta musu rayuwa.

    Wasu alkaluma sun nuna fiye da mutum miliyon 26 ne suke gudun-hijira a duniya.

    Najeriya na cikin kasashen da suke fama da mutanen da rikici ya raba da gidajensu, musamman ma jihar Borno, waddamahukunta suka ce fiye da mutum miliyon daya ne rikicin Boko Haram ya daidaita.

    Ku saurari rahoton Ibrahim Isa inda albarkacin wannan ranaya ziyarci wanisansanin ƴan gudun hijira a Maiduguri.

    Video content

    Video caption: Rahoton Ibrahim Isa
  17. Isra’ila ta ce sabon shugaban Iran abin tsoro ne

    Ebrahim Raisi

    Isra’ila ta bayyana damuwa kan zaɓen Ebrahim Raisi a matsayin sabon shugaban Iran.

    Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Isra’ila, Lior Haiat, ya ce Mista Raisi shi ne shugaban kasar Iran mafi tsaurin ra’ayi da aka taɓa yi.

    Ya yi gargaɗin cewa shugaban zai ci gaba da inganta ayyukan nukiliyar Iran.

    Sannan ya yi kira ga ƙasashen duniya su bayyana damuwa game da zaɓensa a matsayin shugaban Jamhuriyyar Musulunci ta Iran.

    A ranar Asabar aka ayyana Ebrahim Raisi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen Iran, a zaɓen da ake ganin dama shi zai lashe.

    Mista Raisi mai shekara 60, shi ne aƙalin alƙalan Iran wanda ke da tsattsauran ra'ayi. Tuni Amurka ta saka masa takunkumi sannan kuma ana alaƙanta shi da hukunce-hukuncen da aka yanke wa 'yan adawar siyasa.

  18. Ƙarin mutum 51 sun kamu da korona a Najeriya

    Hukumar da ke dakile cutuka masu yaɗuwa NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 51 da suka kamu da korona a Najeriya a ranar Juma'a.

    Alƙalumman sun nuna cewa a jihohi biyar aka samu masu cutar inda a jihar Legas da cutar ta fi yawa aka samu mutum 41, sai jihar River mutum biyar.

    Sauran sun hada da Gombe inda aka samu mutum uku, Abuja mutum daya da Akwa Ibom ma mutum daya.

    ncdc
  19. Maraba

    Muna maku maraba da kasancewa da mu a wannan shafin inda za mu shafe yinin Lahadi muna kawo maku labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Sai ku kasance da mu.