Got a TV Licence?

You need one to watch live TV on any channel or device, and BBC programmes on iPlayer. It’s the law.

Find out more
I don’t have a TV Licence.

Rahoto kai-tsaye

Daga Ahmad Tijjani Bawage

time_stated_uk

  1. Yaudarar Buhari aka yi kan tsarin sauya fasalin kuɗi – Gwamna Yahaya Bello

    Hoton Gwamnan Kogi Yahaya Bello

    Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya zargi waɗanda ya kira tsofaffin mambobin PDP da ke jam'iyyar APC da yaudarar Shugaba Muhammadu Buhari game da sauya fasalin takardun kuɗin ƙasar.

    A yau Juma'a ne Kotun Ƙoli ta bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗi na N200 da N500 da N1,000 har zuwa 31 ga watan Disamba.

    Kotun ta yi hakan ne bayan da a farko babban bankin ƙasar, CBN, ya dakatar da amfani da su bisa umarnin Shugaba Buhari.

    Da yake mayar da martani game da hukuncin a gidan Talabijin na Channels, Gwamna Bello wanda ɗaya ne daga cikin gwamnonin jihohi uku da suka fara shigar da ƙara domin ƙalubalantar gwamnatin tarayya kan shirin, ya bayyana matakin a matsayin maƙarƙashiya.

    Wadda ya ce wasu mambobin jam'iyyarsu ta APC da wasu tsofaffin mambobin PDP ke yi.

    Ya bayyana cewa APC tana nazari kan tsare-tsarenta kafin ta aiwatar da su inda ya ce waɗanda aka fara aiwatarwa ba tare da yin nazari a kansu ba, mafi yawan lokuta suna fuskantar suka.

    Amma a wannan yanayin, mashawartan Shugaba Buhari a ɓangaren tattalin arziki ne suka yaudare shi a cewar gwamnan.

  2. Achraf Hakimi na fuskantar bincike kan zargin fyaɗe

    .

    Ɗan wasan ƙwallon ƙafa na PSG, Achraf Hakimi yana fuskantar bincike sakamakon zargin da aka yi masa na yin fyaɗe.

    Hakimi ya musanta zargin da wata mata mai shekara 24 ta yi cewa ya yi mata fyaɗe a gidansa da ke Paris ranar 25 ga watan Fabarairu.

    Lauyoyin ɗan wasan sun ce zargin ƙoƙari ne na yi masa maƙarƙashiya.

    Ofishin gabatar da ƙara na Nanterre ya ce ana sa ido kan Hakimi kuma an haramta masa yin duk wata hulɗa da matar.

    A cewar lauyansa, Fanny Colin, Hakimi mai shekara 24 "ya musanta dukkanin zarge-zargen da aka yi masa" kuma yana maraba da binciken saboda "yana da damar da zai kare kansa".

    "Ƙungiyar PSG da yake buga wa wasa na goyon bayan ɗan wasanta da ya musanta zarge-zargen kuma yana da yaƙinin za a yi masa adalci," kamar yadda PSG ta bayyana a sanarwar da ta fitar jiya Alhamis.

    Kocin PSG Christophe Galtier ya ƙi cewa komai game da binciken a taron manema labaran da aka yi yau Juma'a.

  3. Gobara ta hallaka mutum 16 a Indonesia

    Hoton jami'an agaji

    Hukumomi a babban birnin ƙasar Indonesia, Jakarta sun ce kimanin mutum 16 ne suka mutu wasu da dama kuma suka ji rauni bayan da wata gobara ta tashi a wata ma'ajiyar mai.

    Gobarar da ta tashi ɗazu da rana ta lalata gidaje da yawa sannan mutane sun tsere abin da ya tilasta aka soma aikin kwashe mutane da ke zaune kusa da wajen.

    Hukumar kashe gobara a birnin ta ce mutum 16 har da yara biyu ne suka mutu sanadin gobarar da ta jikkata kimanin ƙarin mutum 50.

    Galibin waɗanda suka mutu da waɗanda suka jikkata sun samu ƙuna a jikinsu bayan da wutar ta tashi.

    Zuwa yanzu dai ba a iya tantance abin da ya haddasa tashin gobarar ba.

    Babban jami'in soji a yankin ya faɗa wa ƴan jarida cewa suna gudanar da bincike kan musabbabin gobarar.

  4. Ana makokin mutuwar wani ɗan damisa a Iran

    .

    Ƴan Iran suna makokin mutuwar wata damisa da ta zama wata alama ta fata ga masu zanga-zanga adawa da gwamnati.

    Pirouz ta ɗauki hankali a kafafen sada zumunci bayan da ta rayu. Ta mutu ne sanadiyyar matsalar ƙoda a wani asibiti da ke Tehran a watan da ya gabata, lamarin da ya sa ake ta aika saƙon ta'aziyya.

    Damisar ta samu yabo daga masu zanga-zangar ƙin jinin gwamnati da aka soma tun Satumba sakamakon mutuwar wata mata a hannun hukumar Hisba ta ƙasar.

    Tun farko miliyoyin Iraniyawa ne suka fara bibiyar labarin Pirouz a kafafen sada zumunta da kafafen yaɗa labarai.

    Duk da cewa damisa 12 ne kawai ake tunanin suna rayuwa a Iran, ƙasar na ci gaba da zama ɗaya daga cikin wuraren da wannan daba da ke fsukantar barazanar ƙarewa a doron ƙasa, a cewar jami'an Iran.

    A 2022 ne aka mayar da mahaifiyar damisar da ake kira Iran zuwa Touran, wata cibiyar ajiyar namun daji da ke arewa maso yammacin ƙasar inda aka haɗa ta da namijin damisa mai suna Firouz.

  5. Yadda likitoci suka manta almakashin tiyata a cikin wata ƴar Indiya

    .

    Wata mata a jihar Kerala, a kudancin Indiya da ta shafe shekaru tana fama da matsanancin zafi saboda tiyatar da aka yi mata da ba ta yi nasara ba, ta ce har yanzu tana jiran a hukunta likitocin da ke da hannu a lamarin.

    Wakilin BBC Imran Qureshi ya tattauna da ita game da fafutukar da take ta neman a yi mata adalci.

    KK Harshina, mai shekara 31 ta ce ta kasance tana rayuwa ne cikin matsanancin zafi a cikinta tsawon shekaru.

    Sai bayan da hoton cikinta da aka ɗauka a shekarar da ta gabata ya gano almakashi irin na tiyata da aka manta a cikinta.

    "Ba zan iya kwatanta zafin da na ɗanɗana ba tsawon shekara biyar," in ji Ms Harshina.

    An yi wa Ms Harshina wadda take da ƴaƴa uku tiyata ne domin ciro duka jariran.

    Tiyatarta ta ƙarshe kuma an yi mata ne a asibitin koyarwa na Government Medical College a 2017 inda aka ciro ɗa namiji.

    Bayan tiyatar ce kuma ta soma jin raɗaɗi a cikinta, kamar yadda ta ce.

    "Da na bayyana irin zafin da nake ji, likitoci sun faɗa min cewa ina jin haka ne saboda aikin tiyatar da aka yi min karo na uku ne," in ji ta.

    "An kuma faɗa min cewa mata da dama suna kai irin wannan kukan."

    Sai dai bayan da ta ci gaba da fuskantar zafin ta tuntuɓi likitoci da dama.

  6. Tsohon akanta a Najeriya zai sha ɗaurin shekara 21 kan kuɗin 'yan fansho

    .

    An samu wani tsohon akanta a ofishin shugaban ma'aikata na Najeriya, Garba Abdullahi Tahir da laifin wawushe kuɗin fansho da ya kai Naira miliyan 26 inda kuma aka yanke masa hukuncin shekara 21 a gidan yari.

    Hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa tattalin arziki zagon ƙasa a Najeriya ce ta gurfanar da Garba Abdullahi gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja kan wasu laifuka bakwai da ke da alaƙa da almundahana.

    Da yake yanke hukunci, alƙali Inyang Ekwo ya ce EFCC ta tabbatar da tuhumar da take yi wa tsohon akantan inda kuma aka same shi da laifin aikata duka laifukan.

    Mai shari'ar ya yanke masa hukuncin ɗaurin shekara uku-uku a kan dukkanin laifukan bakwai, jumulla ke nan zai shafe shekara bakwai a gidan maza.

    Wata sanarwa da kakakin EFCC, Wilson Uwajaren ya fitar ta ce tun farko wanda ake tuhumar ya musanta aikata laifukan da aka tuhume shi da su.

  7. Burundi za ta tura sojoji domin yaƙar ƴan tawayen Congo

    Burundi

    Burundi ta ce za ta tura kimanin sojoji 100 zuwa Lardin North Kivu a gabashin Jamhuriyar Dumukuraɗiyyar Kongo inda ƙungiyoyin masu riƙe da makamai ke gwabza faɗa.

    Za su haɗu da dakarun gabashin Afirka da suka haɗa da sojoji daga Kenya.

    An tura sojojin a watan Nuwamba sakamakon sake ɓullar ƴan tawayen M23 da ake zargin Rwanda da mara wa baya amma gwamnatin ta musanta.

    Ƴan tawayen na dab da janyewa a ƙarshen watan nan daga yankunan da suka ƙwace.

    A baya dai an gaza cika wa'adin da aka ɗiba, kuma a baya-bayan nan mutanen da ke son sojojin gabashin Afirka su ɗauki wani mataki na murƙushe ƴan tawaye suka gudanar da zanga-zanga a gabashin Congo.

  8. Kotu ta bai wa Atiku da Obi damar duba kayan zaɓen da aka yi amfani da su

    Peter Obi da Atiku Abubakar

    Kotun ɗaukaka ƙara a Abuja ta bai wa ɗan takarar shugaban Najeriya a ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na Labour, Peter Obi damar duba kayayyakin da aka yi amfani da su a zaɓen ranar 25 ga watan Fabarairu.

    Tun farko ƴan takarar ne daban-daban suka miƙa buƙatar neman a ba su damar duba kayayyakin da aka yi amfani da su a babban zaɓen 2023 tare da tilasta wa INEC ta ba su damar ganin kayan aikin da aka yi amfani da su a zaɓen shugaban ƙasar.

    A ranar Laraba 1 ga watan Maris ne Atiku Abubakar ya shigar da tasa ƙarar yayin da Peter Obi kuma ya shigar da tasa ranar Alhamis biyu ga watan.

    Kan haka ne kotun ta umarci hukumar zaɓe ta bai wa ɗan takarar PDP damar duba kayayyakin zaɓen.

    A yau Juma'a kuma kotun ta amsa bukatun 'yan takarar na duba kayan zaɓen sannan kuma su titsiye hukumar zaɓe kan wasu bayanai da za su buƙata.

    Kotun ƙarƙashin mai shari'a Joseph Ikyegh ta bayar da umarnin ne bayan da ta saurari wasu ƙararraki da ƴan takarar biyu suka shigar tare da jam'iyyunsu.

    PDP da LP waɗanda a baya-bayan nan suka yi watsi da sakamakon zaɓen, sun ce samun damar ganin kayayyakin za ta taimaka musu a ƙalubalantar sakamakon zaɓen da suke yi wanda ya ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara.

    A cewar INEC, Tinubu ya ci zaɓen ne da ƙuri'u 8,794,726 inda Atiku Abubakar na PDP yake bi masa da ƙuri'u 6,984,520 sai Obi na Labour Party da ya zo na uku da ƙuri'u 6,101,533.

  9. Jihohi shida sun buƙaci Kotun Koli ta soke zaɓen shugaban ƙasa

    Supreme Court

    Wasu jihohi shida a Najeriya sun kai ƙarar gwamnatin ƙasar zuwa gaban Kotun Koli, inda ta ke buƙatar ta soke zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisar tarayya da aka gudanar a ranar 25 ga watan Febrairu.

    Jihohin sun haɗa Adamawa da Akwa Ibom da Bayelsa da Delta da Edo da kuma Sokoto.

    Sun yi kira ga Kotun Kolin da ta yi amfani da tanade-tanaden doka wajen soke zaɓen duba da irin kura-kurai da kuma zargin tafka maguɗi.

  10. Fashewar bututun mai ta hallaka mutane da dama a Ribas

    Pipeline Explosion

    Mutane da dama ne ake fargabar sun mutu sakamakon fashewar wani abu da ya faru a wani wurin da ake hako ɗanyen mai a anguwar Rumuekpe da ke karamar hukumar Emuoha a jihar Ribas.

    Ana kyautata zaton fashewar ta samo asali ne sakamakon ayyukan masu haramtattun matatun mai da ke aiki a kan bututun mai na Neja Delta a yankin.

    Haka kuma ta yi sanadiyyar asarar rayukan da ba a tantance adadinsu ba da suka haɗa da mata, wasu daga cikinsu ba a iya gane su saboda ƙonewar da suka yi tare kuma da lalata dukiyoyi na miliyoyin nairori.

    Tashar Talabijin ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da sanyin safiyar yau Juma’a, inda ɗaya daga cikin motocin bas ɗauke da ɗanyen mai ta tashi da wuta a lokacin da ta ke kokarin tafiya zuwa wani haramtaccen wurin tace mai a yankin.

    Kakakin Rundunar ’yan sandan Jihar Ribas, Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce tuni jami’an ‘yan sandan sun tafi zuwa yankin domin ba da ɗauki.

  11. 'Yan sanda sun kama mutum 11 da ƙoƙon kan mutane a Ibadan

    Police

    Rundunar 'yan sanda a jihar Oyo, ta ce ta kama wasu mutum 11 a jihar Oyo ɗauke da ƙoƙon kan mutane guda 10 da hanji da kuma sassan jikkuna.

    Mai magana da yawun 'yan sandan jihar, SP Adewale Osifeso, shi ya bayyana wa manema labarai hakan jiya Alhamis.

    Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito kakakin 'yan sandan na cewa sun kama waɗanda ake zargin ne bayan samun bayanan sirri a ranar 22 ga watan Febrairu.

    Adewale ya ce sun yi dirar miƙiya kan masu yin safi da sassan jikunan mutane ne da kuma sayar da shi a wani yanki mai suna Orita-Aperin a Ibadan, inda ya ce mutanen sun amsa laifin da ake zarginsu da shi.

    Ya ƙara da cewa wasu daga cikin ƙoƙon kan mutanen tono su aka yi daga cikin kaburbura, inda wasu kuma aka ciresu bayan kashe mutane.

  12. An soki 'yan sandan Habasha kan dukan mutanen da suka fito fareti

    Ethiopia

    Kungiyar kare hakkin ɗan adam da gwamnatin Habasha ta naɗa, ta soki jami'an tsaron ƙasar kan duka da kuma amfani da harsashi a kan dandazon mutane a Addis Ababa, babban birnin ƙasar.

    Ta ce an kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu da dama.

    A ranar Alhamis ne mutane suka taru domin bikin tunawa da nasarar da ƙasar ta samu kan masu mamaya na Italiya a ƙarni 19 a lokacin fafatawa ta Adwa.

    An fesawa mutane hayaki mai sa kwalla a ɗaya daga cikin birnin ƙasar na mabiya cocin Orthodox mai tarihi.

    Hukumomi a Habasha sun yi sake na barin mutane hawa kan tituna don yin zanga-zanga tun bayan da mutane suka fito don nuna fushinsu kan rabewar cocin nan mai tasiri na Orthodox.

    An toshe yawancin kafafen sada zumunta na tsawon makonni a ƙasar.

  13. A shirye Amurka ta ke wajen taimaka wa Ukraine - Blinken

    G20 MEETING

    Sakataren harkokin wajen Amurka ya shaida wa ministan harkokin wajen Rasha cewa a shirye ƙasarsa ta ke ta ci gaba da taimakon Ukraine domin kare ƙasarta.

    Anthony Blinken da Sergei Lavrov sun yi takaitacciyar tattaunawa a wurin taron kolin ƙasashen G-20 da ke gudana a Indiya.

    Mai magana da yawun Mista Blinken, Ned Price ya shaida wa BBC cewa ƙasashen duniya da Majalisar Dinkin Duniya duk sun nuna rashin amincewa da mamayar, inda ya ce Ukraine ta bukaci taimakon, dan haka Blinken bai boye wa Lavrov matsayar Amurka kan batun yakin ba.

    An dai kammala taron ba tare da an fidda sanarwar karshe kan matsayar kasashen ba.

  14. An yanke wa jagoran 'yan adawa a Cambodia ɗaurin shekara 27 a kurkuku

    Kem Sokha

    An haramtawa jagoran 'yan adawa a Cambodia Kem Sokha duk wani abu da ya shafi siyasa tare daurin shekaru 27 a gidan kaso kan laifin cin amanar kasa.

    Ana kallon Kem Sokhaa matsayin babban mai kalubalantar gwamnatin firaiminista Hun Sen.

    An zarge shi da hada kai da gwamnatocin kasashen waje, da jam'iyyarsa ta Cambodia National Rescue Party da aka kawo karshenta a 2017.

    Sai dai a Kem Sokha ya musanta zarge-zargen da ake ma sa.

    Amurka ta yi gaggawar kin amincewa da hukuncin, wanda ya zo watanni kadan gabannin kasar Cambodia ta gudanar da zabe.

  15. Kotu a Amurka ta samu wani da laifin kashe matarsa

    Alex Murdaugh

    Kotu a Amurka ta samu wani fitaccen lauya a ƙasar da hannu dumu-dumu kan kisan matar shi da kuma ɗan su a katafaren gidan da suke ciki.

    Lokacin da alkalin ke yanke hukuncin, Alex Murdaugh bai wani nuna karaya ko damuwa ba.

    Alkalin ya ce an samu mista Alex da laifin mallakar bindiga da kisan matarsa da kuma ɗansa.

    An yanke masa hukuncin ɗaurin shekara 30 a gidan kaso.

    A watan Yunin 2021 ne ya harɓe iyalansa, a gidansu da ke South Carolina.

  16. Somaliland ta zargi dakarun Puntland da shirin kai mata hari

    Somaliland ta yi gargadi game da harin da sojoji daga yankin Puntland mai makwaɓtaka da Somaliya za su kai wa yankunanta, inda ta sha alwashin kare kanta daga duk wani hari da za a kai mata.

    A cikin wata sanarwa da ta fitar, ma'aikatar tsaron Somaliland ta ce ta samu sahihan bayanan sirri da ke nuna cewa jami'an tsaron PSF da na 'yan sandan ruwa na Puntland na shirin kai wa sojojinta hari cikin 'yan kwanaki masu zuwa.

    Somaliland ta ce tana ɗaukar barazanar da muhimmanci kuma ta ɗauki dukkan matakan da suka dace don kare al'ummarta da yankunanta.

    Har ila yau, ta buƙaci ƙasashen duniya da su yi Allah wadai da "aikin zaluncin da bai dace ba" da kuma goyon bayan hakkinsu na kare kai.

    Ana dai kallon matakin a matsayin yaɗuwar tashin hankali cikin watanni biyu da suka gabata a yankunan da ake takaddama a kai waɗanda dukkannin Puntland da Somaliland ke iƙirarin mallakarsu.

    An fitar da sanarwar ne sa'o'i bayan da hukumomin yankin suka yanke hukuncin cewa mayakan kabilanci da ke yaki da sojojin Somaliland na samun taimako daga dakarun Puntland da na Somaliya.

  17. Nasarar Tinubu nufin Allah ne – Aisha Buhari

    Aisha Buhari

    Mai ɗakin shugaban Najeriya, Aisha Buhari, ta kwatanta nasarar Bola Tinubu na jam'iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasa da aka kammala da cewa nufi ne na Allah.

    Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya ruwaito cewa Aisha Buhari ta bayyana haka ne lokacin da ta karɓi bakuncin uwar gidan zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Sanata Oluremi Tinubu da mai ɗakin zaɓaɓɓen mataimakin shugaban ƙasa, Hajiya Nana Shettima, a wani ziyarar godiya da suka kai mata.

    Ta ce "duk da bambance-bambance na ra'ayi, mu karɓi nasarar da cewa nufi ne na Allah".

    Tun da farko Sanata Oluremi Tinubu ta faɗa wa mutane da suka taru cewa sun je faɗar shugaban ƙasa ne domin gode wa mai ɗakin shugaba Buhari saboda irin goyon baya da ta basu wajen ganin APC ta samu nasara a zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar.

    Zaman ya samu halartar matan wasu gwamnonin APC da ƙawayen matar shugaban ƙasar.

  18. Tinubu zai koma gidan zaɓaɓɓen shugaban ƙasa a Abuja

    Tinubu

    Zaɓaɓɓen shugaban Najeriya, Bola Tinubu, zai koma da zama a gidan zaɓaɓɓen shugaban ƙasa da ke Abuja, babban birnin ƙasar, gabanin bikin rantsar da shi, a cewar tawagar yakin neman zaɓensa.

    "Zaɓaɓɓen shugaban ƙasa zai koma gidan tsaro, a Maitama, inda zai shafe watanni biyu a ciki, daga nan kuma zai koma fadar shugaban ƙasa," in ji sanarwar a cikin wani sakon Twitter.

    Ba a fayyace lokacin da Mista Tinubu zai koma wurin ba.

    Zaɓaɓɓen shugaban ƙasar zai gudanar da muhimman taruka a wurin, kamar yadda wata jaridar ƙasar ta ruwaito.

    Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari mai barin gado ya koma ama a gidan kafin rantsar da shi a watan Mayun 2015.

    An ayyana Mista Tinubu na jam’iyyar APC mai mulki a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa da kashi 37%.

    Sai dai, 'yan adawa sun ce za su kalubalanci sakamakon a kotu.

    Suna da kwanaki 21 daga ranar da aka bayyana sakamakon zaɓen domin kalubalantar sakamakon a kotun kolin Najeriya.

  19. SDP ta ce ba za ta kalubalanci sakamakon zaɓen Tinubu ba

    SDP

    Jam'iyyar SDP mai adawa a Najeriya ta ce ba za ta kalubalanci sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da hukumar zaɓe ta sanar ba wanda ya bai wa Bola Tinubu nasara.

    Shugaban jam'iyyar Shehu Gabam, shi ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Abuja jiya Alhamis.

    "Duk da cewa an samu kura-kurai a zaɓen, SDP ba za ta kalubalanci nasarar Tinubu ba na jam'iyyar APC a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasa,'' in ji Gabam.

    Ya ce jam'iyyar ta yi na'am da zaɓin 'yan ƙasa kuma sun amince da sakamakon zaɓen.